< Amos 6 >
1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
»Gorje tistim, ki so v udobju na Sionu in zaupajo v samarijsko goro, ki se imenujejo vodje narodov, h katerim je prihajala Izraelova hiša!
2 Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
Prečkajte v Kalne in poglejte in od tam pojdite v veliki Hamát. Potem pojdite dol v Gat Filistejcev. Mar so boljši kakor ta kraljestva? Je njihova meja večja kakor vaša meja?
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
Vi, ki zli dan polagate daleč stran in sedežu nasilja naredite, da pride blizu,
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
ki ležite na posteljah iz slonovine in se iztegujete na svojih ležiščih in jeste jagnjeta iz tropa in teleta iz srede hleva,
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
ki monotono pojete na zvok lire in si izmišljate glasbene instrumente, podobno kakor David;
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
ki pijete vino v skledicah in se mazilite z vodilnimi mazili. Toda niso užaloščeni zaradi Jožefove stiske.
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
Zato bodo sedaj šli ujeti s prvimi, ki gredo ujeti in gostija tistih, ki so se iztegovali, bo odstranjena.
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
Gospod Bog je prisegel pri samem sebi, « govori Gospod, Bog nad bojevniki, »preziram odličnost Jakoba in sovražim njegove palače, zato bom izročil mesto, z vsem, kar je v njem.
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
In zgodilo se bo, če tam ostane deset ljudi v eni hiši, da bodo umrli.
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
In njegov stric ga bo vzdignil in tisti, ki ga sežiga, da odnese kosti iz hiše in rekel bo tistemu, ki je pri straneh hiše: › Je tam še kdo s teboj?‹ Ta pa bo rekel: ›Ne.‹ Potem bo rekel: ›Molči, kajti ne smemo omenjati Gospodovega imena.‹
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
Kajti glej, Gospod zapoveduje in veliko hišo bo udaril z vrzelmi in majhno hišo z razpokami.
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
Mar bodo konji tekli po skali? Ali bo tam kdo oral z voli? Kajti sodbo ste obrnili v žolč in sad pravičnosti v pikasti mišjak.
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
Vi, ki se veselite v ničevi stvari, ki pravite: ›Mar nismo s svojo lastno močjo k sebi vzeli rogov?‹
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”
Toda glejte, zoper vas bom dvignil narod, oh Izraelova hiša, « govori Gospod, Bog nad bojevniki, »in stiskali vas bodo od vstopanja v Hamát, do reke iz divjine.«