< Amos 6 >

1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
Ak vai, tiem, kas droši dzīvo Ciānā un bez bēdām uz Samarijas kalna, tiem vareniem pirmajā tautā, pie kuriem nāk tie no Israēla nama.
2 Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
Ejat uz Kalni un skatāties, un no turienes ejat uz Hamatu, to lielo pilsētu, tad noejat uz Gadu Fīlistos, vai tās ir labākas nekā šīs valstis, jeb vai viņu robežas lielākas nekā jūsu robežas.
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
Jūs, kam šķiet nelaimes dienu tālu esam un kas tuvu ceļat varasdarba krēslu,
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
Kas guļat uz ziloņkaulu gultām un staipāties savās guļās un ēdat jērus no ganāmā pulka un barotos teļus no laidaru vidus,
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
Kas pūšat somastabules un izdomājat mūzikas rīkus kā Dāvids,
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
Kas vīnu dzerat no kausiem un svaidāties ar visdārgāko eļļu, bet nebēdājaties par Jāzepa vainu!
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
Tādēļ tie nu ies cietumā paši pirmie starp cietumniekiem, un plītnieku kliegšana mitēsies.
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
Tas Kungs Dievs ir zvērējis pie savas dvēseles, saka Tas Kungs, tas Dievs Cebaot: Man riebj Jēkaba lepnība un Es ienīstu viņa skaistos namus, tādēļ Es to pilsētu nodošu ar visu, kas tur iekšā.
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
Un notiks, ja tur desmit vīri būs atlikuši vienā namā, tie mirs.
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
Un kad ko ņems viņa svainis vai viņa dedzinātājs, un iznesīs tos kaulus no nama un sacīs uz to, kas nama kambarī: vai tur vēl kāds pie tevis? Un tas sacīs: nav neviena. Tad viņš sacīs: ciet klusu! Jo Tā Kunga vārdu nebūs pieminēt.
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
Jo redzi, Tas Kungs dod pavēli, un sitīs to lielo namu, ka sagrūs, un to mazo namu, ka sadrups.
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
Vai zirgi var skriet pa klintīm? Vai tur virsū var art ar vēršiem? Jo jūs esat pārvērtuši tiesu par žulti un taisnības augļus par vērmelēm?
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
Jūs, kas priecājaties par nieku un sakāt: Vai mēs caur savu stiprumu sev neesam varu dabūjuši?
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”
Jo redzi, pret jums, jūs Israēla nams, saka Tas Kungs, tas Dievs Cebaot, Es celšu vienu tautu, - un tā jūs nospaidīs no Hamatas ceļa līdz tuksneša upei.

< Amos 6 >