< Amos 6 >
1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
Woe to those who are at ease in Zion, and to those who are secure in the hill country of Samaria, the notable men of the best of the nations, to whom the house of Israel comes for help!
2 Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
Your leaders say, “Go to Kalneh and look; from there go to Hamath, the great city; then go down to Gath of the Philistines. Are they better than your two kingdoms? Is their border larger than your border?”
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
Woe to those who put off the day of disaster and make the throne of violence come near.
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
They lie on beds of ivory and lounge on their couches. They eat lambs from the flock and calves from the stall.
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
They sing foolish songs to the music of the harp; they improvise on instruments as David did.
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
They drink wine from bowls and anoint themselves with the finest oils, but they do not grieve over the ruin of Joseph.
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
So they will now go into exile with the first exiles, and the feasts of those who lounge about will pass away.
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
“I, the Lord Yahweh, have sworn by myself —this is the declaration of the Lord Yahweh, the God of hosts, I detest the pride of Jacob; I hate his fortresses. Therefore I will deliver up the city with all that is in it.”
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
It will come about that if there are ten men left in one house, they will all die.
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
When a man's relative comes to take their bodies up—the one who is to cremate them after bringing the corpses out of the house—if he says to the person in the house, “Is there anyone with you?” What if that person says, “No.” Then he will say, “Be quiet, for we must not mention Yahweh's name.”
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
For, look, Yahweh will give a command, and the big house will be smashed to pieces, and the little house to bits.
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
Do horses run on the rocky cliffs? Does one plow there with oxen? Yet you have turned justice into poison and the fruit of righteousness into bitterness.
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
You who rejoice over Lo Debar, who say, “Have we not taken Karnaim by our own strength?”
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”
“But look, I will raise up against you a nation, house of Israel—this is the declaration of the Lord Yahweh, the God of hosts. They will afflict you from Lebo Hamath to the brook of the Arabah.”