< Amos 6 >

1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
Sorrow awaits who are carefree in Zion, overconfident on the mountain of Samaria! The elite of this, the best of nations, on whom the people of Israel rest their hopes!
2 Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
You say to the people: Cross over to Calneh and see, go from there to Hamath the great, then go down to Gath of the Philistines: Are they better than these kingdoms? Is their territory larger than yours?
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
You push away all thoughts of the evil day, yet have instituted a rule of violence.
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
They lie on ivory couches, sprawl on their divans, eat choice lambs from the flock, and fattened calves from the stall.
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
They idly sing to the sound of the lyre, thinking themselves songwriters like David,
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
they drink bowlfuls of wine, and anoint themselves with the finest of oil. But they do not grieve over the ruin of Joseph.
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
Therefore now they must go into exile at the head of the captives, and hushed will be the revelry of the sprawlers.
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
The Lord God, the Lord, the God of hosts, has sworn by himself: I abhor the pride of Jacob, I hate his palaces, therefore I will deliver up the city and all that is in it to their enemies.
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
If ten people remain in one house, then they will die.
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
When the uncle and another member of the family of a dead man come to carry the body out of the house for burial, they will call to someone in a corner of the house, “Any more there?” and he will answer, “No”, and then he will add, “Be quiet!” – for the name of the Lord must not be mentioned.
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
Look! The Lord is giving the command! He will smash the large house to bits, the small house into fragments.
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
Do horses gallop on crags? Does one plough the sea with oxen? Yet you turn justice into poison weed, and the fruit of righteousness into bitter wormwood.
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
You who are so proud of capturing Lo-debar, who say, “Have we not by our own strength taken Karnaim for ourselves?”
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”
I am now raising up against you, Israel, a nation, says the Lord, the God of hosts. They will oppress you, from the entrance of Hamath to the brook of the Arabah.

< Amos 6 >