< Amos 6 >

1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
Woe to them that are at ease in Zion and trust in the moutaine of Samaria, which were famous at the beginning of the nations: and the house of Israel came to them.
2 Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
Goe you vnto Calneh, and see: and from thence goe you to Hamath the great: then goe downe to Gath of the Philistims: be they better then these kingdomes? or the border of their land greater then your border,
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
Ye that put farre away the euill day, and approch to the seate of iniquitie?
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
They lie vpon beddes of yuorie, and stretch themselues vpon their beddes, and eate the lambes of the flocke, and the calues out of the stall.
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
They sing to the sounde of the viole: they inuent to themselues instruments of musike like Dauid.
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
They drinke wine in bowles, and anoynt themselues with the chiefe ointments, but no man is sory for the affliction of Ioseph.
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
Therefore nowe shall they go captiue with the first that go captiue, and the sorow of them that stretched themselues, is at hand.
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
The Lord God hath sworne by himselfe, saith the Lord God of hostes, I abhorre the excellencie of Iaakob, and hate his palaces: therefore wil I deliuer vp the citie with all that is therein.
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
And if there remaine ten men in one house, they shall die.
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
And his vncle shall take him vp and burne him to cary out the bones out of the house, and shall say vnto him, that is by ye sides of the house, Is there yet any with thee? And he shall say, None. Then shall he say, Holde thy tongue: for we may not remember the Name of the Lord.
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
For behold, the Lord commandeth, and he will smite the great house with breaches, and the litle house with clefts.
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
Shal horses runne vpon the rocke? or wil one plowe there with oxen? for yee haue turned iudgement into gall, and the fruite of righteousnes into wormewood.
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
Ye reioyce in a thing of nought: yee say, Haue not wee gotten vs hornes by our owne strength?
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”
But behold, I wil raise vp against you a nation, O house of Israel, sayeth the Lord God of hostes: and they shall afflict you, from the entring in of Hamath vnto the riuer of the wildernes.

< Amos 6 >