< Amos 6 >
1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, da ku waɗanda kuke ji zama a Dutsen Samariya lafiya ne, ku manyan mutanen ƙasar da take sananniya, waɗanda mutanen Isra’ila suke zuwa!
Ve de trygge i Zion og de sorgløse paa Samarias Bjerg, de navnkundige iblandt det første af Folkene og dem, til hvilke Israels Hus kommer.
2 Ku je Kalne ku dube ta; ku wuce daga can zuwa Hamat-rabba, sa’an nan ku gangara zuwa Gat a Filistiya. Sun fi masarautunku biyu ne? Ƙasarsu ta fi taku girma?
Gaar over til Kalne og ser, og gaar derfra til det store Hamath, og drager ned til Filisternes Gath! mon de ere lykkeligere end disse Riger? eller mon deres Landemærke er større end eders Landemærke?
3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan muguwar rana kuna kuma jawo mulkin tashin hankali kusa.
I, som vise den onde Dag bort og bringe Volds Sæde til at komme nærmere!
4 Kuna kwanciya a kan gadajen da aka yi musu shimfiɗar hauren giwa kuna mimmiƙe a kan kujerunku. Kuna cin naman ƙibabbun raguna da na ƙosassun’yan maruƙa.
Folk, som sove paa Elfenbens Senge og række sig paa deres Leje, og som æde Lam af Hjorden og Kalve fra Fedestalden;
5 Kuna kaɗa molayenku yadda Dawuda ya yi kuna ƙirƙiro waƙoƙi a kan kayan kaɗe-kaɗe.
som fremkunstle Toner efter Psalteren og, som David, optænke sig Strengeleg;
6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi kuna kuma shafa mai mafi kyau, amma ba kwa baƙin ciki game da kangon da Yusuf ya zama.
som drikke Vin af Skaaler og salve sig med den ypperste Olie, men føle ikke Smerte over Josefs Brøst!
7 Saboda haka za ku zama na farkon da za su tafi zaman bauta; bukukkuwanku da shagulgulanku za su ƙare.
Derfor skulle de nu bortføres, fremmest iblandt de bortførte, og Frydesangen af dem, som rækkede sig, skal ophøre.
8 Ubangiji Mai Iko Duka da kansa ya rantse, Ubangiji Allah Maɗaukaki ya furta, “Ina ƙyamar girman kan Yaƙub, ba na kuma son kagarunsa; zan ba da birnin da duk abin da yake cikinta.”
Den Herre, Herre har svoret ved sig selv, siger Herren, Zebaoths Gud: Jeg afskyr Jakobs Stolthed og hader hans Paladser, derfor vil jeg prisgive Staden og dens Fylde.
9 Ko da mutum goma ne suka ragu a gida guda, su ma za su mutu.
Og det skal ske, hvis der i eet Hus bliver ti Mænd tilovers, da skulle de dø;
10 In kuma wani dangi ya shiga don yă fitar da gawawwakin yă ƙone ya kuwa tambayi wani wanda yake ɓoye a can, yana cewa, “Akwai wani tare da kai?” Ya kuwa ce, “Babu,” sai yă ce, “Kul! Kada mu ambaci sunan Ubangiji.”
og en Mands næste Slægtning eller den, der besørger hans Begravelse, skal tage ham for at udbære Benene af Huset; og han skal sige til den, som er i det inderste af Huset: Mon der endnu er flere hos dig? og denne skal svare: Der er ingen! saa skal han sige: Tys! thi det er ikke Tid nu at paakalde Herrens Navn.
11 Gama Ubangiji ya ba da umarni, zai kuma ragargaza babban gidan nan kucu-kucu ƙaramin gidan kuwa zai yi rugu-rugu da shi.
Thi se, Herren byder, og han slaar det store Hus i Splinter og det lille Hus i Stykker.
12 Dawakai sukan yi gudu a kan duwatsu? Wani yana iya yin noma a teku da shanun noma? Amma ga shi kun mai da gaskiya ta zama dafi amfanin adalci kuma ya zama ɗaci,
Mon Heste løbe paa Klippen? mon man pløjer der med Øksne? thi I have omvendt Retten til Galde og Retfærdighedens Frugt til Malurt.
13 ku da kuke murna saboda an ci Lo Debar da yaƙi kuka kuma ce, “Ba da ƙarfinmu ne muka ƙwace Karnayim ba?”
I som glædes ved det, som intet er, og som sige: Have vi ikke ved vor Styrke taget os Horn?
14 Gama Ubangiji Allah Maɗaukaki ya ce, “Zan sa wata ƙasa ta tayar muku, ya ku gidan Isra’ila, wadda za tă matsa muku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba.”
Thi se, jeg rejser et Folk imod eder, Israels Hus! siger Herren, Zebaoths Gud, og de skulle trænge eder fra Hamath af og indtil Bækken paa den slette Mark.