< Amos 5 >
1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Poslušajte to besedo, ki jo vzdigujem zoper vas, celó žalostinko, oh Izraelova hiša.
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
Devica Izrael je padla, ne bo več vstala, zapuščena je na svoji zemlji, tam ni nikogar, ki bi jo vzdignil.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
Kajti tako govori Gospod Bog: »Mestu, ki je šlo ven po tisoč, jih preostane sto in tistemu, ki je šlo naprej po sto, jih preostane deset, Izraelovi hiši.«
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
Kajti tako govori Gospod Izraelovi hiši: »Iščite me in boste živeli,
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
toda ne iščite Betela niti ne vstopajte v Gilgál in ne prečkajte v Beeršébo, kajti Gilgál bo zagotovo šel v ujetništvo in Betel bo prišel v nič.
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Iščite Gospoda in boste živeli, da ne izbruhne kakor ogenj v Jožefovi hiši in jo použije in tam ne bo nikogar, da bi jo gasil v Betelu.
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
Vi, ki prevračate sodbo v grenkobo in opuščate pravičnost na zemlji,
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
iščite njega, ki določa sedem zvezd in Orion in obrača senco smrti v jutro in dan mrači z nočjo, ki kliče po vodah morja in jih izliva na obličje zemlje, Gospod je njegovo ime,
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
ki jača oplenjenega zoper močnega, tako da bo oplenjeni prišel zoper trdnjavo.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
Sovražijo tistega, ki graja v velikih vratih in prezirajo tistega, ki govori iskreno.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Ker kakor je torej vaše mendranje nad revnim in vi od njega jemljete bremena žita; zgradili ste hiše iz klesanega kamna, toda ne boste prebivali v njih; sadili ste prijetne vinograde, toda ne boste pili vina od njih.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
Kajti jaz poznam vaše mnogotere prestopke in vaše mogočne grehe; stiskajo pravičnega, jemljejo podkupnino in v velikih vratih revne odvračajo od njihove pravice.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Zato bo v tem času razsoden molčal, kajti to je hud čas.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Iščite dobro in ne zla, da boste lahko živeli in tako bo Gospod, Bog nad bojevniki, z vami, kakor ste govorili.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Sovražite zlo in ljubite dobro in vzpostavite sodbo v velikih vratih. Morda bo Gospod, Bog nad bojevniki, milostljiv Jožefovemu preostanku.«
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
Zato Gospod, Bog nad bojevniki, Gospod, tako govori: »Tarnanje bo na vseh ulicah in na vseh glavnih cestah bodo govorili: ›Ojoj! Ojoj!‹ in poklicali bodo poljedelca, da žaluje in tiste, ki so vešči objokovanja, da tarnajo.
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
In v vseh vinogradih bo tarnanje, kajti jaz pojdem skozte, « govori Gospod.
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
»Gorje vam, ki si želite Gospodovega dneva! Čemu vam bo to? Dan Gospodov je tema in ne svetloba.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
Kakor če je človek pobegnil pred levom in ga je srečal medved; ali odšel v hišo in svojo roko naslonil na zid in ga je pičila kača.
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
Mar ne bo Gospodov dan tema in ne svetloba? Celo zelo temen in nobenega svetlikanja v njem?
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
Sovražim, preziram vaše praznične dni in nočem povonjati vaših slovesnih zborov.
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
Čeprav mi darujete žgalne daritve in jedilne daritve, jih ne bom sprejel niti se ne bom oziral na mirovne daritve vaših debelih živali.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Šum svojih pesmi vzemi proč od mene, kajti ne bom poslušal melodije tvojih lir.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
Temveč naj sodba teče dol kakor vode in pravičnost kakor mogočen vodotok.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
Mar ste mi darovali klavne daritve in jedilne daritve štirideset let v divjini, oh hiša Izraelova?
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
Toda nosili ste šotor svojega Moloha in Kijúna, svojih podob, zvezdo svojega boga, kar ste si naredili zase.
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
Zatorej vam bom povzročil, da greste v ujetništvo onkraj Damaska, « govori Gospod, čigar ime je Bog nad bojevniki.