< Amos 5 >
1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Dengarlah hai umat Israel! Aku hendak menyanyikan bagimu sebuah nyanyian duka:
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
Telah jatuh Israel yang masih perawan, ia tak akan bangkit lagi! Di atas tanahnya sendiri ia dibiarkan, tak ada yang membantu ia berdiri.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
TUHAN Yang Mahatinggi berkata, "Sebuah kota di Israel mengerahkan seribu orang prajurit, tapi yang kembali hanyalah seratus; kota yang lain mengerahkan seratus orang, yang kembali hanya sepuluh."
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
TUHAN berkata kepada umat Israel, "Kembalilah kepada-Ku, maka kamu akan hidup.
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
Jangan pergi ke Bersyeba untuk berbakti. Jangan mencari Aku di Betel, sebab Betel akan lenyap. Jangan juga pergi ke Gilgal, sebab penduduk kota itu akan diangkut ke pembuangan."
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Kembalilah kepada TUHAN, maka kamu akan hidup. Jika kamu tidak kembali kepada-Nya, Ia akan datang seperti api yang menjalar dan membakar habis orang Israel. Di Betel tak seorang pun dapat memadamkan api itu.
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
Celakalah kamu, kamu yang memutarbalikkan keadilan dan memperkosa hak orang!
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
Tuhanlah yang membuat bintang-bintang di angkasa--bintang Belantik dan bintang Kartika. Ia mengubah gelap menjadi terang dan siang menjadi malam; air dari laut dituangkan-Nya ke daratan. Yang melakukan semua itu nama-Nya ialah TUHAN.
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
Ia membinasakan orang berkuasa bersama pertahanan mereka.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
Kamu membenci orang yang menentang ketidakadilan dan yang berbicara benar dalam pengadilan.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Kamu menindas orang miskin dan gandumnya kamu rampas. Karena itu kamu tidak akan tinggal di dalam rumah-rumahmu yang mewah, yang telah kamu bangun itu. Kamu tidak akan minum anggur dari kebun-kebun anggur yang kamu tanami.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
Aku tahu betapa besar kejahatanmu dan betapa banyak dosamu. Kamu menindas orang baik; kamu menerima sogok dan membiarkan orang miskin diperlakukan tidak adil di pengadilan.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Karena perbuatanmu itu, maka orang-orang yang bijaksana merasa lebih baik diam saja pada masa yang jahat seperti itu.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Berusahalah berbuat baik dan jangan berbuat jahat, supaya kamu hidup. Maka TUHAN Yang Mahakuasa akan sungguh-sungguh tinggal di antara kamu seperti yang kamu katakan.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Bencilah yang jahat, cintailah yang baik, dan tegakkanlah keadilan. Mungkin TUHAN akan mengasihani orang-orang yang tersisa dari bangsa Israel.
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
TUHAN Yang Mahakuasa berkata, "Di jalan-jalan kota, orang akan meratap dan berkeluh-kesah karena sedih. Bahkan para petani akan dipanggil untuk turut menangis bersama orang-orang yang dibayar untuk meratapi orang mati.
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
Di semua kebun anggur, orang akan meratap karena Aku datang dan menghukum kamu. Aku, TUHAN, telah berbicara."
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
Sungguh celakalah kamu yang merindukan hari TUHAN! Apa gunanya hari itu bagimu? Hari itu hanya merupakan hari yang gelap, bukan hari yang terang bagimu.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
Keadaannya seperti orang yang melarikan diri dari singa, tapi bertemu dengan beruang. Atau seperti orang yang pulang ke rumah dan bertopang dengan tangannya ke tembok, lalu dipagut ular!
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
Hari TUHAN memang mendatangkan kegelapan, bukan terang--hari mendung yang suram.
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
TUHAN berkata, "Aku benci dan muak melihat perayaan-perayaan agamamu!
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
Kalau kamu membawa kurban bakaran dan kurban gandum, Aku tidak akan menerimanya. Aku tak mau menerima binatang-binatangmu yang gemuk-gemuk itu yang kamu persembahkan kepada-Ku sebagai kurban perdamaian.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Hentikan nyanyian-nyanyianmu yang membisingkan itu; Aku tak mau mendengarkan permainan kecapimu.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
Lebih baik, berusahalah supaya keadilan mengalir seperti air, dan kejujuran seperti sungai yang tak pernah kering.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
Hai umat Israel, pada waktu Aku menuntun kamu melalui padang gurun empat puluh tahun lamanya, Aku tidak menuntut persembahan dan kurban dari kamu.
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
Tapi sekarang kamu menyembah Sakut yang kamu anggap rajamu itu, dan Kewan, bintang yang kamu dewakan itu. Karena itu arca-arca yang telah kamu buat itu harus kamu angkut sendiri.
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
Apabila Aku membuang kamu ke suatu negeri yang lebih jauh dari Damsyik. Aku TUHAN yang bernama Allah Yang Mahakuasa telah berbicara."