< Amos 5 >

1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Hear the word this which I [am] lifting up on you a lamentation O house of Israel.
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
She has fallen not she will repeat to rise [the] virgin of Israel she has been abandoned on own land her there not [is one who] raises up her.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
For thus he says [the] Lord Yahweh the city which goes out a thousand it will have left a hundred and which goes out a hundred it will have left ten of [the] house of Israel.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
For thus he says Yahweh to [the] house of Israel seek me and live.
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
And may not you seek Beth-el and Gilgal not you must go and Beer Sheba not you must pass over for Gilgal certainly it will go into exile and Beth-el it will become trouble.
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Seek Yahweh and live lest he should rush like fire [the] house of Joseph and it will consume and not [one who] extinguishes [it] [will belong] to Beth-el.
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
O those [who] turn into wormwood justice and righteousness to the ground they thrust down.
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
[the] maker of Pleiades and Orion and [the one who] turns into morning deep darkness and day night he makes dark the [one who] summons [the] waters of the sea and he poured out them on [the] surface of the earth [is] Yahweh name his.
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
The [who] causes to flash devastation on [the] strong and devastation on a fortress it will come.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
They hate in the gate [one who] reproves and [one who] speaks blameless they abhor.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Therefore because trample you on [the] poor and a portion of grain you take from him houses of hewn [stone] you have built and not you will dwell in them vineyards of delight you have planted and not you will drink wine their.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
For I know many transgressions your and numerous sins your O opposers of [the] righteous O takers of ransom and needy [people] in the gate they turn aside.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Therefore the prudent [person] at the time that he will be silent for [is] a time evil it.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Seek good and may not [it be] evil so that you will live and it may be thus Yahweh God of hosts [will be] with you just as you have said.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Hate evil and love good and set up in the gate justice perhaps he will show favor to Yahweh God of hosts [the] remnant of Joseph.
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
Therefore thus he says Yahweh God of hosts [the] Lord [will be] in all [the] open places wailing and in all [the] streets people will say alas! alas! and people will call a farmer to mourning and wailing to [those who] know lamentation.
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
And [will be] in all [the] vineyards wailing for I will pass in midst your he says Yahweh.
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
Woe to! those [who] desire [the] day of Yahweh why? this to you [the] day of Yahweh it [will be] darkness and not light.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
Just as he flees someone from before the lion and it meets him the bear and he goes the house and he leans hand his on the wall and it bites him the snake.
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
¿ Not [be] darkness [will] [the] day of Yahweh and not light and gloomy and not brightness [will belong] to it.
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
I hate I reject feasts your and not I delight in assemblies your.
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
That except you will offer up to me burnt offerings and grain offerings your not I will accept [them] and [the] peace offering of fatlings your not I will pay attention to.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Remove from with me [the] noise of songs your and [the] music of lyres your not I will listen to.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
And it may roll on like water justice and righteousness like a wadi ever-flowing.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
¿ Sacrifices and grain offering[s] did you bring near to me in the wilderness forty year[s] O house of Israel.
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
And you will lift up Sikkuth king your and Kiyyun images your [the] star of gods your which you made for yourselves.
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
And I will send into exile you from beyond Damascus he says [is] Yahweh God of hosts name his.

< Amos 5 >