< Amos 5 >

1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Hear ye this word which I take up for a lamentation over you, O house of Israel:
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
The virgin of Israel is fallen, she shall no more rise; she is cast down upon her land, there is none to raise her up.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
For thus saith the Lord GOD: The city that went forth a thousand shall have a hundred left, and that which went forth a hundred shall have ten left, of the house of Israel.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
For thus saith the LORD unto the house of Israel: Seek ye Me, and live;
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
But seek not Beth-el, nor enter into Gilgal, and pass not to Beer-sheba; for Gilgal shall surely go into captivity, and Beth-el shall come to nought.
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Seek the LORD, and live — lest He break out like fire in the house of Joseph, and it devour, and there be none to quench it in Bethel —
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
Ye who turn judgment to wormwood, and cast righteousness to the ground;
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
Him that maketh the Pleiades and Orion, and bringeth on the shadow of death in the morning, and darkeneth the day into night; that calleth for the waters of the sea, and poureth them out upon the face of the earth; the LORD is His name;
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
That causeth destruction to flash upon the strong, so that destruction cometh upon the fortress.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
They hate him that reproveth in the gate, and they abhor him that speaketh uprightly.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Therefore, because ye trample upon the poor, and take from him exactions of wheat; ye have built houses of hewn stone, but ye shall not dwell in them, ye have planted pleasant vineyards, but ye shall not drink wine thereof.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
For I know how manifold are your transgressions, and how mighty are your sins; ye that afflict the just, that take a ransom, and that turn aside the needy in the gate.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Therefore the prudent doth keep silence in such a time; for it is an evil time.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Seek good, and not evil, that ye may live; and so the LORD, the God of hosts, will be with you, as ye say.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Hate the evil, and love the good, and establish justice in the gate; it may be that the LORD, the God of hosts, will be gracious unto the remnant of Joseph.
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
Therefore thus saith the LORD, the God of hosts, the Lord: Lamentation shall be in all the broad places, and they shall say in all the streets: 'Alas! alas!' and they shall call the husbandman to mourning, and proclaim lamentation to such as are skilful of wailing.
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
And in all vineyards shall be lamentation; for I will pass through the midst of thee, saith the LORD.
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
Woe unto you that desire the day of the LORD! Wherefore would ye have the day of the LORD? It is darkness, and not light.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
As if a man did flee from a lion, and a bear met him; and went into the house and leaned his hand on the wall, and a serpent bit him.
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
Shall not the day of the LORD be darkness, and not light? Even very dark, and no brightness in it?
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
I hate, I despise your feasts, and I will take no delight in your solemn assemblies.
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
Yea, though ye offer me burnt-offerings and your meal-offerings, I will not accept them; neither will I regard the peace-offerings of your fat beasts.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Take thou away from Me the noise of thy songs; and let Me not hear the melody of thy psalteries.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
But let justice well up as waters, and righteousness as a mighty stream.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
Did ye bring unto Me sacrifices and offerings in the wilderness forty years, O house of Israel?
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
So shall ye take up Siccuth your king and Chiun your images, the star of your god, which ye made to yourselves.
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
Therefore will I cause you to go into captivity beyond Damascus, saith He, whose name is the LORD God of hosts.

< Amos 5 >