< Amos 5 >
1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Počujte ovu riječ što je iznosim protiv vas, naricaljku, dome Izraelov:
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
Pade i više neće ustati djevica izraelska. Na tlu svojem ona leži, nikog da je digne.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
Jer ovako govori Jahve Gospod domu Izraelovu: u gradu iz kojeg izlažaše tisuća, ostat će stotina, iz kojeg izlažaše stotina, ostat će ih deset.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
Jer ovako govori Jahve domu Izraelovu: “Tražite i živjet ćete.
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
Ne tražite Betela, ne idite u Gilgal, ne putujte u Beer Šebu, jer će Gilgal bit odveden u izgnanstvo, a Betel će se prometnuti u ništa.
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Tražite Jahvu i živjet ćete, il' će ko' oganj zahvatiti kuću Josipovu i sažeć' je, a u Betelu nikog da plamen ugasi.”
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
Jao onima koji pravdu pretvaraju u pelin, u prah bacaju poštenje!
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
On napravi Vlašiće i Štapce, on obrće mrak u zoru, a dan u najglušu noć. On saziva morske vode i valja ih preko lica zemlje. Jahve mu je ime.
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
Nenadano šalje pustoš na tvrđavu i utvrdi propast nosi.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
Mrze čovjeka što na vratima pravdu dijeli i grde onog što zbori pošteno.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Stoga, jer gazite siromaha, dižući od njega porez u žitu - u kućama što ih sazdaste od tesanika nikad živjet' nećete; iz ljupkih vinograda što ih posadiste nikad nećete piti vina.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
Jer znam mnoge vaše zločine, i vaše grijehe pregoleme: tlačite pravednika i primate mito, odbijajuć' siromaha na gradskim vratima.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Mudrac šuti u ovo vrijeme, jer vremena su tako zla.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Tražite dobro, a ne zlo, da biste živjeli, i da Jahve, Bog nad Vojskama, odista s vama bude kao što velite da jest.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Mrzite zlo, ljubite dobro, držite pravicu na gradskim vratima, pa će se možda Jahve, Bog nad Vojskama, smilovat' ostatku Josipovu.
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
Stog ovako govori Jahve, Bog nad Vojskama, Gospod: “Na svakom će trgu biti kuknjava, po svim će ulicama zapomagati: 'Jao! Jao!' Težake će sazvat' da jauču, narikače da nariču,
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
bit će jauk u svakom vinogradu, jer ću proći posred tebe” - veli Jahve.
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
“Jao vama što žudite za danom Jahvinim! Što će vam biti dan Jahvin? Tama, a ne svjetlost.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
Bit će vam k'o onom što uteče lavljim raljama, a sretne ga medvjed; koji uđe u kuću i stavi ruku na zid, a ujede ga zmija.
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
Neće li dan Jahvin biti tama, a ne svjetlost? Mrklina, a ne sunčan sjaj?
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
Mrzim i prezirem vaše blagdane i nisu mi mile vaše svečanosti.
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
Paljenice kad mi prinosite, prinosnice mi vaše nisu mile, na pričesnice se od ugojenih telaca vaših i ne osvrćem.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Uklonite od mene dreku svojih pjesama, neću da slušam zvuke vaših harfa.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
Pravda nek' poteče kao voda i pravica k'o bujica silna.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
Prinosiste li mi žrtve i prinos u pustinji četrdeset godina, dome Izraelov?
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
Nosit ćete Sikuta, svoga kralja, i Kevana, boga svoga, likove što ih sebi napraviste,
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
dok vas budem odvodio onkraj Damaska,” govori Jahve - Bog nad Vojskama njemu je ime.