< Amos 4 >
1 Ku kasa kunne ga wannan, ya ku shanun Bashan a kan Dutsen Samariya, ku matan da kuke cin zalin matalauta, kuke kuma danne matalauta, kuna kuma ce wa mazanku, “Ku kawo mana abin sha!”
»Poslušajte to besedo, ve bašánske krave, ki ste na samarijski gori, ki stiskate uboge, ki drobite pomoči potrebne, ki svojim gospodarjem pravite: ›Prinesite in naj pijemo.‹
2 Ubangiji Mai Iko Duka ya rantse da tsarkinsa. “Tabbatacce lokaci yana zuwa da za a jawo ku da ƙugiyoyi, na ƙarshenku za a kama da ƙugiyar kifi.
Gospod Bog je prisegel pri svoji svetosti, da, glejte, nad vas bodo prišli dnevi, ko vas bo odvedel proč s kavlji in vaše potomstvo s trnki.
3 Dukanku za ku wuce ta kai tsaye ta inda katangar ta tsage, za a jefar da ku a Harmon,” in ji Ubangiji.
Šle boste ven pri vrzelih, vsaka krava pri tisti, ki je pred njo, in vrgle jih boste v palačo, « govori Gospod.
4 “Ku tafi Betel ku yi ta aikata zunubi; ku je Gilgal ku ƙara yin zunubi. Ku kawo hadayunku kowace safiya, zakkarku kowace shekara uku.
»Prihajate v Betel in grešite, pri Gilgálu množite prestopek in vsako jutro prinašajte svoje klavne daritve in svoje desetine po treh letih
5 Ku ƙona burodinku mai yisti kamar hadaya ta godiya, ku yi fariya game da hadayunku na yarda rai, ku yi taƙama game da su, ya ku Isra’ilawa, gama abin da kuke jin daɗin aikata ke nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
in darujte žrtev zahvaljevanja s kvasom in razglašajte in objavljajte prostovoljne daritve, kajti to vam je všeč, oh vi, Izraelovi otroci, « govori Gospod Bog.
6 “Na bar ku da yunwa a kowace birni, da kuma rashin abinci a kowane gari, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
»In tudi jaz sem vam dal čistost zob po vseh vaših mestih in pomanjkanje kruha po vseh vaših krajih. Vendar se niste vrnili k meni, « govori Gospod.
7 “Na kuma hana muku ruwan sama tun shuke-shuken suna wata uku kafin lokacin girbi. Na sa aka yi ruwan sama a wani gari, sai na hana a yi a wani gari. Wata gona ta sami ruwan sama; wata gona kuma ta bushe.
»In tudi jaz sem zadržal dež pred vami, ko je bilo še tri mesece do žetve in mu dal, da dežuje nad enim mestom in dal, da ne dežuje nad drugim mestom. Na en kos je deževalo, kos pa, na katerega ni deževalo, se je posušil.
8 Mutane suna tangaɗi daga gari zuwa gari suna neman ruwa amma ba su sami isashen ruwan sha ba, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
Tako so dva ali tri mesta tavala k enemu mestu, da pijejo vodo, toda niso bila nasičena. Vendar se niste vrnili k meni, « govori Gospod.
9 “Sau da yawa na ɓata gonakinku da fumfuna da kuma cuta. Fāri suka cinye itatuwanku na inabi da na ɓaure, da na zaitun duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
»Udaril sem vas s kvarjenjem in plesnijo. Ko so se množili vaši vrtovi in vaši vinogradi in vaša figova drevesa in vaše oljke, jih je požrla kosmata gosenica. Vendar se niste vrnili k meni, « govori Gospod.
10 “Na aiko muku annoba yadda na yi a Masar. Na karkashe samarinku da takobi, tare da kamammun dawakanku. Na cika hancinku da warin sansaninku, duk da haka ba ku juyo gare ni ba” in ji Ubangiji.
»Med vas sem poslal kužno bolezen po načinu iz Egipta. Vaše mladeniče sem umoril z mečem in vaše konje odvedel proč in storil sem, da se smrad vaših taborov vzdigne do vaših nosnic, vendar se niste vrnili k meni, « govori Gospod.
11 “Na hallaka waɗansunku kamar yadda na hallaka Sodom da Gomorra. Kuna kama da itace mai cin wutar da na cire daga cikin wuta, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
»Uničil sem nekatere izmed vas, kakor je Bog razdejal Sódomo in Gomóro in ste bili kakor kos tlečega lesa, izvlečenega iz gorenja, vendar se niste vrnili k meni, « govori Gospod.
12 “Saboda haka ga abin da zan yi da ku, ya Isra’ila, don kuwa zan yi muku haka, sai ku yi shirin gamuwa da Allahnku, ya Isra’ila.”
»Zato ti bom tako storil, oh Izrael in ker ti bom to storil, se pripravi, da srečaš svojega Boga, oh Izrael.
13 Shi wanda ya yi duwatsu, ya halicci iska, ya kuma bayyana wa mutum tunaninsa, shi wanda ya juya safiya ta zama duhu yana takawa a wurare masu tsawo na duniya, Ubangiji Allah Maɗaukaki ne sunansa.
Kajti glej, tisti ki oblikuje gore in ustvarja veter in razglaša človeku, kaj je njegova misel, ki dela jutranjo temo in mendra na visokih krajih zemlje. Gospod, Bog nad bojevniki, je njegovo ime.«