< Amos 4 >
1 Ku kasa kunne ga wannan, ya ku shanun Bashan a kan Dutsen Samariya, ku matan da kuke cin zalin matalauta, kuke kuma danne matalauta, kuna kuma ce wa mazanku, “Ku kawo mana abin sha!”
Klausiet šo vārdu, Basanas govis, kas Samarijas kalnā, kas nospaida mazos, satriec nabagus, kas uz saviem kungiem saka: nesiet šurp, ka dzeram.
2 Ubangiji Mai Iko Duka ya rantse da tsarkinsa. “Tabbatacce lokaci yana zuwa da za a jawo ku da ƙugiyoyi, na ƙarshenku za a kama da ƙugiyar kifi.
Tas Kungs Dievs ir zvērējis pie Sava svētuma: redzi, dienas nāks pār jums, ka jūs aizvilks ar kāšiem un jūsu beidzamos ar zivju makšķerēm,
3 Dukanku za ku wuce ta kai tsaye ta inda katangar ta tsage, za a jefar da ku a Harmon,” in ji Ubangiji.
Un jūs iziesiet caur mūru plaisām, ikviena taisni projām, un tapsiet nomestas pret Armonu, saka Tas Kungs.
4 “Ku tafi Betel ku yi ta aikata zunubi; ku je Gilgal ku ƙara yin zunubi. Ku kawo hadayunku kowace safiya, zakkarku kowace shekara uku.
Ejat uz Bēteli un grēkojiet! (Ejat) uz Gilgalu un vairojiet pārkāpšanu! Un nesiet savus upurus rītos, savas desmitās(tiesas) ik trešo dienu,
5 Ku ƙona burodinku mai yisti kamar hadaya ta godiya, ku yi fariya game da hadayunku na yarda rai, ku yi taƙama game da su, ya ku Isra’ilawa, gama abin da kuke jin daɗin aikata ke nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Un kvēpinājiet pateicības upurus no raudzēta, un izsauciet labprātības upurus, liekat to dzirdēt! Jo tā tas jums patīk, Israēla bērni, saka Tas Kungs Dievs.
6 “Na bar ku da yunwa a kowace birni, da kuma rashin abinci a kowane gari, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
Tāpēc es arīdzan jūsu zobiem esmu devis mieru visās jūsu pilsētās un maizes trūkumu visās jūsu vietās; tomēr jūs pie Manis neesat atgriezušies, saka Tas Kungs.
7 “Na kuma hana muku ruwan sama tun shuke-shuken suna wata uku kafin lokacin girbi. Na sa aka yi ruwan sama a wani gari, sai na hana a yi a wani gari. Wata gona ta sami ruwan sama; wata gona kuma ta bushe.
Un arī lietu Es jums esmu aizturējis, kad vēl trīs mēneši bija līdz pļaujamam laikam, un esmu licis līt pār vienu pilsētu, bet pār otru ne, viens zemes gabals aplija, bet otrs gabals sakalta, kur lietus nelija.
8 Mutane suna tangaɗi daga gari zuwa gari suna neman ruwa amma ba su sami isashen ruwan sha ba, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
Un divas, trīs pilsētas vilkās uz vienu pilsētu, ūdeni dzert, bet nedabūja nodzerties; taču jūs pie Manis neesat atgriezušies, saka Tas Kungs.
9 “Sau da yawa na ɓata gonakinku da fumfuna da kuma cuta. Fāri suka cinye itatuwanku na inabi da na ɓaure, da na zaitun duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
Es jūs esmu sitis ar bulu un ar rūsu, un siseņi ēda visu, kas aug jūsu dārzos un jūsu vīna dārzos un uz jūsu vīģes kokiem un eļļas kokiem, taču jūs pie Manis neesat atgriezušies, saka Tas Kungs.
10 “Na aiko muku annoba yadda na yi a Masar. Na karkashe samarinku da takobi, tare da kamammun dawakanku. Na cika hancinku da warin sansaninku, duk da haka ba ku juyo gare ni ba” in ji Ubangiji.
Es esmu sūtījis mēri jūsu vidū, kā Ēģiptes zemē, Es nokāvu jūsu jaunekļus caur zobenu un liku jūsu zirgus aizvest, un jūsu karaspēka smaržai Es liku uzkāpt jūsu nāsīs; taču jūs pie Manis neesat atgriezušies, saka Tas Kungs.
11 “Na hallaka waɗansunku kamar yadda na hallaka Sodom da Gomorra. Kuna kama da itace mai cin wutar da na cire daga cikin wuta, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
Es esmu sūtījis postu jūsu vidū, kā Dievs postījis Sodomu un Gomoru un jūs bijāt kā pagale izrauta no uguns, taču jūs neesat atgriezušies pie Manis, saka Tas Kungs.
12 “Saboda haka ga abin da zan yi da ku, ya Isra’ila, don kuwa zan yi muku haka, sai ku yi shirin gamuwa da Allahnku, ya Isra’ila.”
Tādēļ Es tev tā darīšu, Israēl! Kad Es tev tā gribu darīt, nu tad sataisies, Israēl, savam Dievam pretim!
13 Shi wanda ya yi duwatsu, ya halicci iska, ya kuma bayyana wa mutum tunaninsa, shi wanda ya juya safiya ta zama duhu yana takawa a wurare masu tsawo na duniya, Ubangiji Allah Maɗaukaki ne sunansa.
Jo redzi, kas taisa kalnus, rada vēju un cilvēkam dara zināmu, kas viņa domās, kas par rīta gaismu dara tumsu un staigā pār zemes augstumiem, Kungs Dievs Cebaot ir Viņa vārds.