< Amos 3 >

1 Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
Чујте реч коју говори Господ за вас, синови Израиљеви, за све племе које сам извео из земље мисирске, говорећи:
2 “Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
Само вас познах између свих племена земаљских, зато ћу вас походити за сва безакоња ваша.
3 Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
Хоће ли двојица ићи заједно, ако се не састану?
4 Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
Хоће ли рикнути лав у шуми, ако нема лова? Хоће ли лавић пустити глас свој из пећине своје, ако не ухвати шта?
5 Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
Хоће ли птица пасти у мрежу на земљу, ако нема замке? Хоће ли се дигнути мрежа са земље, ако се ништа не ухвати?
6 Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
Хоће ли труба трубити по граду, а народ да не дотрчи уплашен? Хоће ли бити несрећа у граду, а Господ да је не учини?
7 Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
Јер Господ Господ не чини ништа не откривши тајне своје слугама својим пророцима.
8 Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
Кад лав рикне, ко се неће бојати? Кад Господ рече, ко неће пророковати?
9 Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
Огласите по дворовима азотским и по дворовима у земљи мисирској, и реците: Скупите се на горе самаријске и видите велике нереде у њој, и насиље у њој.
10 “Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
Не знају чинити право, говори Господ, сабирају благо насиљем и грабежом у дворима својим.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
Зато овако вели Господ Господ: Непријатељ је око земље и обориће ти силу твоју, и оплениће се дворови твоји.
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
Овако вели Господ: Као кад пастир истргне из уста лаву две ноге или крај од уха, тако ће се истргнути синови Израиљеви који седе у Самарији на углу од одра и накрај постеље.
13 “Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Чујте и засведочите у дому Јаковљевом, говори Господ Господ Бог над војскама.
14 “A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
Кад походим Израиља за грехе његове, тада ћу походити и олтаре ветиљске, и одбиће се рогови олтару и пашће на земљу.
15 Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.
И ударићу кућу зимну и летњу кућу, и пропашће куће од слонове кости, и нестаће великих кућа, говори Господ.

< Amos 3 >