< Amos 3 >

1 Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
Klausiet šo vārdu, ko Tas Kungs runā uz jums, Israēla bērni, proti uz visām tām ciltīm, ko Es no Ēģiptes zemes esmu izvedis, sacīdams:
2 “Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
Es jūs vien esmu atzinis no visām zemes tautām, tādēļ Es pie jums piemeklēšu visus jūsu noziegumus.
3 Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
Vai divi gan kopā staigā, ja tie papriekš nav saderējušies?
4 Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
Vai lauva mežā rūc, kad viņam laupījuma nav? Vai jauns lauva balsi paceļ no savas alas, kad neko nav gūstījis?
5 Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
Vai putns iekrīt valgā pie zemes, kur valga priekš viņa nav? Vai valgs no zemes ceļas, ar ko nekas nav gūstīts?
6 Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
Vai pilsētā bazūnē ar bazūni, un ļaudis neiztrūkstās? Vai kāda nelaime notiek pilsētā, ko Tas Kungs nedara?
7 Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
Tiešām, Tas Kungs Dievs nekā nedara, kad viņš savu noslēpumu neparāda saviem kalpiem, tiem praviešiem.
8 Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
Kad lauva rūc, kas nebītos? Tas Kungs Dievs runā, kam nebūtu jāsludina?
9 Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
Liekat to dzirdēt Ašdodas skaistos namos un Ēģiptes zemes pilīs un sakāt: sapulcinājaties uz Samarijas kalniem un redziet tos lielos trokšņus viņas vidū, un tos nospaidītos viņas starpā.
10 “Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
Jo tie nezin darīt, kas tiesa(taisnība), saka Tas Kungs, krādami netaisnību un varas darbu savās pilīs.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
Tāpēc Tas Kungs Dievs tā saka: spaidi zemei visapkārt! Un viņš nogāzīs tavu stiprumu, un tavi skaistie nami taps izpostīti.
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
Tā saka Tas Kungs: kā gans izrauj no lauvas rīkles divus stilbus vai kādu auss gabaliņu, tā Israēla bērni tiks izglābti, kas Samarijā sēž gultas kaktā uz Damaskus pēļa.
13 “Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Klausiet un dodiet liecību Jēkaba namam, saka Tas Kungs Dievs, tas Dievs Cebaot:
14 “A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
Tai dienā, kad Es Israēla pārkāpumus pie viņa piemeklēšu, tad Es piemeklēšu Bēteles altārus, un tie altāra ragi taps nocirsti un kritīs zemē.
15 Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.
Un Es sitīšu tiklab ziemas pili kā vasaras pili, un tie ziloņkaulu nami ies bojā, un daudz nami taps izpostīti, saka Tas Kungs.

< Amos 3 >