< Amos 3 >
1 Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
Kuulkaa tämä sana, jonka Herra on puhunut teitä vastaan, te israelilaiset, koko sitä sukukuntaa vastaan, jonka minä olen johdattanut Egyptin maasta, sanoen:
2 “Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
Ainoastaan teidät minä olen valinnut kaikista maan sukukunnista; sentähden minä kostan teille kaikki teidän pahat tekonne.
3 Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
Kulkeeko kaksi yhdessä, elleivät ole keskenänsä sopineet?
4 Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
rjyykö leijona metsässä, ellei sillä ole raadeltavaa? Kiljuuko nuori leijona luolastansa, ellei se ole saalista saanut?
5 Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
Käykö lintu maassa paulaan, ellei sen varalle ole pyydystä pantu? Nouseeko paula maasta saaliin siihen tarttumatta?
6 Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
Puhalletaanko pasunaan kaupungissa, niin ettei kansa peljästy? Tahi tapahtuuko kaupungissa onnettomuutta, jota ei Herra ole tuottanut?
7 Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
Sillä ei Herra, Herra, tee mitään ilmoittamatta salaisuuttaan palvelijoillensa profeetoille.
8 Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
Leijona ärjyy: kuka ei pelkäisi? Herra, Herra puhuu: kuka ei ennustaisi?
9 Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
Julistakaa Asdodin palatseille ja Egyptin maan palatseille ja sanokaa: Kokoontukaa Samarian vuorille ja katsokaa, mikä suuri meteli on sen keskellä ja mikä sorto sen sisällä.
10 “Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
He eivät ymmärrä tehdä sitä, mikä oikein on, sanoo Herra; he kokoovat väkivaltaa ja sortoa palatseihinsa.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
Sentähden, näin sanoo Herra, Herra: Vihollinen on oleva kaikkialla maassa, ja hän kukistaa sinun linnoituksesi, ja sinun palatsisi ryöstetään.
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
Näin sanoo Herra: Niinkuin paimen saa pelastetuksi leijonan kidasta pari sääriluuta tai kappaleen korvaa, niin pelastuu israelilaisiakin, niitä, jotka istuvat Samariassa sohvankulmassa ja kirjosilkkisellä leposijalla.
13 “Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Kuulkaa ja todistakaa Jaakobin heimoa vastaan, sanoo Herra, Herra, Jumala Sebaot:
14 “A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
Sinä päivänä, jona minä kostan Israelille hänen rikoksensa, minä kostan myös Beetelin alttareille, niin että alttarinsarvet hakataan irti ja putoavat maahan.
15 Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.
Ja minä sorran maahan talvihuoneen ja kesähuoneen, ja norsunluuhuoneet kukistuvat, ja paljoista huoneista tulee loppu, sanoo Herra.