< Amos 2 >

1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
Nea Awurade se ni: “Moab ayɛ bɔne bebree ama no atra so, ɛno nti, merennan mʼabufuw. Ɔhyew Edomhene nnompe, maa ɛdan nsõ.
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
Mede ogya bɛto Moab mu, na ahyew Keriot aban. Moab bɛhwe ase wɔ huuyɛ, ɔko nteɛteɛmu ne torobɛnto nnyigyei mu.
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
Mɛsɛe ne hene na makunkum ne mmapɔmma aka ne ho,” sɛnea Awurade se ni.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
Nea Awurade se ni: “Yuda ayɛ bɔne bebree ama no atra so, ɛno nti, merennan mʼabufuw. Wɔapo Awurade mmara no na wɔanni nʼahyɛde so efisɛ atoro anyame no ama wɔafom ɔkwan no, anyame a wɔn nenanom dii akyi no.
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
Mede ogya bɛto Yuda mu na ahyew Yerusalem aban.”
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
Nea Awurade se ni: “Israel ayɛ bɔne bebree ama no atra so, ɛno nti, merennan mʼabufuw. Wɔtɔn atreneefo de gye dwetɛ, ne ahiafo de gye mpaboa.
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
Wotiatia ahiafo so te sɛnea wɔyɛ fam mfutuma na wɔma atɛntrenee bɔ mmɔborɔfo. Agya ne ne ba ne ɔbea baako da de gu me din kronkron no ho fi.
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
Wɔdeda afɔremuka biara ho wɔ wɔn awowa ntama so. Wɔn anyame fi mu no, wɔnom nsa a wɔagye sɛ mmaratode.
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
“Mesɛee Amorifo no wɔ wɔn anim, ɛwɔ mu sɛ wɔwoware te sɛ sida. Wɔn ho nso yɛ den sɛ odum. Nanso mesɛee nʼaba wɔ ne soro, ne ne ntin wɔ nʼase.
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
Miyii mo fii Misraim, na midii mo anim mfirihyia aduanan wɔ sare so sɛnea mede Amorifo asase bɛma mo.
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
Miyiyii mo mmabarima no bi yɛɛ wɔn adiyifo, ne mo mmerante ebinom sɛ Naserefo. Na ɛnte saa ana, Israelfo?” Nea Awurade bisa ni.
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
“Nanso momaa Naserefo no nom nsa na mohyɛɛ adiyifo no sɛ wɔnnhyɛ nkɔm.
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
“Na afei, mɛdwerɛw mo sɛnea teaseɛnam a aduan ayɛ no ma mia asase no.
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
Ahoɔharefo rentumi nguan. Ahoɔdenfo rennya ahoɔden, na ɔkofo rennya ne ti nnidi mu.
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
Agyantowfo rentumi nnyina nea ogyina. Asraafo ahoɔharefo rentumi nguan, na ɔpɔnkɔsotefo rentumi mpere ne nkwa.
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
Mpo akofo akokodurufo de adagyaw beguan wɔ saa da no,” sɛnea Awurade se ni.

< Amos 2 >