< Amos 2 >

1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Moab, yea, for four, I will not turn away the punishment thereof; because he burned the bones of the king of Edom into lime.
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
But I will send a fire upon Moab, and it shall devour the palaces of Kerioth; and Moab shall die with tumult, with shouting, and with the sound of the trumpet;
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
and I will cut off the judge from the midst thereof, and will slay all the princes thereof with him, saith Jehovah.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Judah, yea, for four, I will not turn away the punishment thereof; because they have rejected the law of Jehovah, and have not kept his statutes, and their lies have caused them to err, after which their fathers did walk.
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
But I will send a fire upon Judah, and it shall devour the palaces of Jerusalem.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
Thus saith Jehovah: For three transgressions of Israel, yea, for four, I will not turn away the punishment thereof; because they have sold the righteous for silver, and the needy for a pair of shoes—
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
they that pant after the dust of the earth on the head of the poor, and turn aside the way of the meek: and a man and his father go unto the [same] maiden, to profane my holy name:
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
and they lay themselves down beside every altar upon clothes taken in pledge; and in the house of their God they drink the wine of such as have been fined.
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
Yet destroyed I the Amorite before them, whose height was like the height of the cedars, and he was strong as the oaks; yet I destroyed his fruit from above, and his roots from beneath.
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
Also I brought you up out of the land of Egypt, and led you forty years in the wilderness, to possess the land of the Amorite.
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
And I raised up of your sons for prophets, and of your young men for Nazirites. Is it not even thus, O ye children of Israel? saith Jehovah.
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
But ye gave the Nazirites wine to drink, and commanded the prophets, saying, Prophesy not.
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
Behold, I will press [you] in your place, as a cart presseth that is full of sheaves.
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
And flight shall perish from the swift; and the strong shall not strengthen his force; neither shall the mighty deliver himself;
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
neither shall he stand that handleth the bow; and he that is swift of foot shall not deliver [himself]; neither shall he that rideth the horse deliver himself;
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
and he that is courageous among the mighty shall flee away naked in that day, saith Jehovah.

< Amos 2 >