< Amos 2 >
1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
上主這樣說:「為了摩阿布再三再四犯罪,我不收回成命,因為他們曾將厄東的骨骸焚化成灰。
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
我必將火投於摩阿布,燒盡克黎約特的王宮;摩阿布必在騷嚷、吶喊和號角聲中滅亡。
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
我必由其中消滅民長,將她的一切長官同她一起殺死」──上主說。
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
上主這樣說:「為了猶大再三再四犯罪,我不收回成命,因為他們離背了上主的法律,沒有遵守衪的誡命;他們祖先所追隨的邪神,使他們走入了岐途。
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
我必把火投於,燒盡耶路撒冷的王官」
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
上主這樣說:「為了以色列再三再四犯罪,我不收回成命,因為他們為了銀錢出賣人;為一雙鞋,出賣無辜的人。
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
他們把窮人的頭踏在塵土裏,侵奪卑微人的權利;兒子與父親走近同一少女,以致褻瀆我的聖名;
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
他們靠近每個祭壇,躺在抵押者的衣服上,在他們的神廟內喝剝削來的酒。
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
是我由你們面前消滅了阿摩黎人,他們雖高大似香柏,堅固如橡樹,但我仍從樹上摘去了果實,由樹下拔出了根子。
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
是我由埃及國領你們上來,四十年之久引你們經過曠野,使你們佔領了阿摩黎人的國土。
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
是我從你們的子孫中立了一些人為先知,由你們少年中選拔了一些人作獻身者。以色列子民,是不是這樣呢﹖──上主的斷語。
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
但是,你們竟叫獻身者喝酒,又吩咐先知說:「別傳神言! 」
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
看,我要使你們腳下的地搖蕩,好像車搖蕩一樣,
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
以致疾行者無法逃遁,強有力者無法施展,武士救不了自己,
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
弓手不能屹立,捷足者不能逃脫,騎馬者不能自救。
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
在那一天,武士中最勇敢的,也僅能赤身逃走」──上主的斷語。