< Amos 1 >
1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
Šie ir Amosa, Tekoas avju gana, vārdi, ko viņš ir redzējis pār Israēli Uzijas, Jūda ķēniņa, dienās, un Jerobeama, Jehoas dēla, Israēla ķēniņa, dienās, divus gadus priekš tās zemes trīcēšanas.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
Un viņš sacīja: Tas Kungs rūc no Ciānas un paceļ Savu balsi no Jeruzālemes, ka ganības bēdājās, un Karmeļa galva nokalst.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
Tā saka Tas Kungs: treju vai četru Damaskus pārkāpumu dēļ - to Es nenovērsīšu, - tāpēc ka tie Gileādu kūluši ar asiem dzelzs spriguļiem,
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
Tāpēc Es sūtīšu uguni Azaēļa namā, tas aprīs BenHadada skaistās pilis.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
Un Es salauzīšu Damaskus aizšaujamo un izdeldēšu tos iedzīvotājus no Avenas ielejas un to, kas scepteri tur no BetEdenas; un Sīrijas ļaudis taps aizvesti uz Ķiru, saka Tas Kungs.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Tā saka Tas Kungs: triju vai četru Gacas pārkāpumu dēļ, - to Es nenovērsīšu, - tādēļ ka tie (Manus ļaudis) lielā pulkā aizveduši, tos nodot Edomam,
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
Tādēļ Es sūtīšu uguni Gacas mūros, tas aprīs viņas skaistos namus.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Un Es izdeldēšu tos iedzīvotājus no Ašdodas, un, kas scepteri tur, no Askalonas, un Es griezīšu Savu roku pret Ekronu, ka bojā ies viss Fīlistu atlikums, saka Tas Kungs Dievs.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Tā saka Tas Kungs: treju vai četru Tirus pārkāpumu dēļ, - to Es nenovērsīšu, - tāpēc ka tie Manus ļaudis lielā pulkā nodevuši Edomam un nav pieminējuši brāļu derību,
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
Tāpēc Es sūtīšu uguni Tirus mūros, un tas aprīs viņa skaistos namus.
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Tā saka Tas Kungs: triju vai četru Edoma pārkāpumu dēļ, - to Es nenovērsīšu, - tāpēc ka viņš savu brāli ar zobenu vajājis, un savu mīlestību iznīcinājis un savā bardzībā arvien plosās un patur mūžam savas dusmas,
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
Tāpēc Es sūtīšu uguni Temanā, tas aprīs Bocras skaistos namus.
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Tā saka Tas Kungs: triju vai četru Amona bērnu pārkāpumu dēļ - to Es nenovērsīšu, - tāpēc ka tie Gileādas grūtās sievas uzšķērduši savas robežas izplest,
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
Tāpēc Es iededzināšu uguni Rabas mūros, tas aprīs viņas skaistos namus, kara dienas kliegšanā un vētras dienas aukā.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
Un viņu ķēniņš ies cietumā ar saviem lielkungiem, saka Tas Kungs.