< Amos 1 >

1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
Paroles d'Amos, qui était parmi les bergers de Tekoa, et qu'il vit concernant Israël, au temps d'Ozias, roi de Juda, et au temps de Jéroboam, fils de Joas, roi d'Israël, deux ans avant le tremblement de terre.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
Il dit: « Yahvé rugira de Sion, et faire entendre sa voix de Jérusalem; et les pâturages des bergers seront en deuil, et le sommet du Carmel se flétrira. »
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
Yahvé dit: « Pour trois transgressions de Damas, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, car ils ont battu Galaad avec des instruments de fer;
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
mais je vais envoyer un feu dans la maison de Hazaël, et il dévorera les palais de Ben Hadad.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
Je briserai la barre de Damas, et a exterminé l'habitant de la vallée de l'Aven, et celui qui tient le sceptre de la maison d'Eden; et le peuple de Syrie ira en captivité à Kir, » dit Yahvé.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Yahvé dit: « Pour trois transgressions de Gaza, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, car ils ont emmené en captivité toute la communauté, pour les livrer à Edom;
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
mais j'enverrai un feu sur le mur de Gaza, et il dévorera ses palais.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
J'exterminerai l'habitant d'Asdod, et celui qui tient le sceptre d'Ashkelon; et je tournerai ma main contre Ekron; et le reste des Philistins périra, » dit le Seigneur Yahvé.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Yahvé dit: « Pour trois transgressions de Tyr, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment; car ils ont livré toute la communauté à Edom, et ne s'est pas souvenu de l'alliance fraternelle;
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
mais j'enverrai un feu sur la muraille de Tyr, et il dévorera ses palais. »
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Yahvé dit: « Pour trois transgressions d'Edom, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, parce qu'il a poursuivi son frère avec l'épée et de rejeter toute pitié, et sa colère se déchaînait sans cesse, et il a gardé sa colère pour toujours;
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
mais j'enverrai un feu sur Théman, et elle dévorera les palais de Bozrah. »
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Yahvé dit: « Pour trois transgressions des enfants d'Ammon, oui, pour quatre, Je ne détournerai pas son châtiment, car ils ont éventré les femmes enceintes de Gilead, afin qu'ils puissent élargir leur frontière.
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
Mais je vais allumer un feu dans la muraille de Rabba, et il dévorera ses palais, avec des cris au jour de la bataille, avec une tempête au jour du tourbillon;
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
et leur roi ira en captivité, lui et ses princes ensemble, » dit Yahvé.

< Amos 1 >