< Amos 1 >

1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
This is the message that [Yahweh] gave to [me], Amos. I am a (shepherd/man who takes care of sheep). I am from [near] Tekoa [town south of Jerusalem]. I received this message about Israel in a vision two years before the [big] earthquake. It was when Uzziah was the king of Judah, and Jeroboam, the son of [King] Jehoash, was the king of Israel.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
This is what Yahweh said: “I will roar [like a lion] [MET]; when I speak from Zion [Hill in] Jerusalem [DOU], my voice will [resemble the sound of] thunder. [When that happens], the pastures where you shepherds [take care of] your sheep will dry up, and [the grass] on top of Carmel [Mountain] will (wither/become brown) [because I will cause that no rain will fall].”
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
This is [also] what Yahweh said [to me]: “[I will punish the people of] Damascus, [the capital of Syria, ] because of the many sins that they have committed; I will not [change my mind about punishing them] [MTY], because [the cruel things that they did to the people of the] Gilead [region] [were like] [MET] people threshing grain using sledges [that have (iron teeth/sharp iron nails) in them].
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
I will cause a fire to burn the palace [that King] Hazael [built and lived in], the fortress where [his son King] Ben-Hadad [also] lived.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
I will cause the gates of Damascus to be broken [down]; I will get rid of the king who rules in Aven Valley and the one who rules in Beth Eden. And the people of Syria will be captured and taken to the Kir [region where they originally lived].”
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Yahweh [also] said this [to me]: “[I will punish the people of the cities in Philistia]: [I will punish the people of] Gaza [city] because of the many sins that they have committed; I will not change my mind about punishing them, because they captured large groups of people and took them to Edom and sold them to become the slaves of [the people of] Edom.
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
I will cause a fire to completely burn the walls of Gaza and [also] destroy its fortresses.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I will get rid of the king of Ashdod [city] and the king who rules [MTY] in Ashkelon [city]. I will [also] strike/punish [the people of] Ekron [city], and [all] the people of Philistia who are still alive will be killed.”
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Yahweh [also] said this [to me]: “[I will punish the people of] Tyre [city] because of the many sins that they have committed; I will not change my mind about punishing them, because they [also] captured large groups of our people and took them to Edom, disregarding the treaty of friendship that they had made [with your rulers].
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
So I will cause a fire to completely burn the walls of Tyre and [also] destroy its fortresses.”
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Yahweh [also] said this [to me]: “I will punish [the people of] Edom because of the many sins that they have committed; I will not change my mind about punishing them, because they pursued the people [of Israel], who descended from Esau’s [brother Jacob, and killed them] with swords; they did not act mercifully toward them at all. They were extremely angry [with the people of Israel], and they continued to be angry [with them].
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
I will cause a fire to burn Teman [district in Edom] and completely burn the fortresses of Bozrah, [the biggest city in Edom].”
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Yahweh [also] said this [to me]: “I will punish [the people of] Ammon because of the many sins that [they] have committed; I will not change my mind about punishing them, because [their soldiers even] ripped open [the bellies of] pregnant women [when their army attacked] the Gilead [region] to gain more territory.
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
I will cause a fire to [completely] burn the walls around Rabbah [city] and completely burn its fortresses. During that battle, [their enemies] will shout loudly and the fighting will be [like] [MET] a fierce/raging wind/storm.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
[After the battle], the king [of Ammon] and his officials will be (exiled/forced to go to another country).”

< Amos 1 >