< Amos 1 >

1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
The words of Amos, who was among the shepherds of Tekoa, which he saw about Israel in the days of Uzziah king of Judah, and in the days of Jeroboam the son of Joash king of Israel, two years before the earthquake.
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
And he said: The Lord will roar from Zion, and from Jerusalem he will utter his voice. And the beautiful pastures have mourned, and the top of Carmel has become dry.
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
Thus says the Lord: For three wicked deeds of Damascus, and for four, I will not convert it, in so far as they have threshed Gilead into iron wagons.
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
And I will send fire onto the house of Hazael, and it will devour the houses of Ben-hadad.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
And I will shatter the crowbar of Damascus, and I will destroy the inhabitants of the camp of the idol and the holder of the scepter of the house of pleasure; and the people of Syria will be transferred to Cyrene, says the Lord.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Thus says the Lord: For three wicked deeds of Gaza, and for four, I will not convert it, in so far as they have carried out an excellent captivity, so as to enclose them in Idumea.
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
And I will send a fire onto the wall of Gaza, and it will devour its buildings.
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And I will destroy the inhabitant from Ashdod, and the holder of the scepter of Ashkelon. And I will turn my hand against Ekron, and the remainder of the Philistines will perish, says the Lord God.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Thus says the Lord: For three wicked deeds of Tyre, and for four, I will not convert it, in so far as they have completed an excellent captivity in Idumea and have not considered the bond among brothers.
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
And I will send a fire onto the wall of Tyre, and it will devour its buildings.
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Thus says the Lord: For three wicked deeds of Edom, and for four, I will not convert him, in so far as he has been pursuing his brother with the sword and has outraged his brother’s compassion, and he has gone beyond his anger and has held onto his indignation until the end.
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
I will send a fire onto Teman, and it will devour the buildings of Bozrah.
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Thus says the Lord: For three wicked deeds of the sons of Ammon, and for four, I will not convert him, in so far as he has cut up the pregnant women of Gilead, so as to expand his limits.
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
And I will ignite a fire on the wall of Rabbah. And it will devour its buildings, with wailing on the day of war, and with a whirlwind on the day of commotion.
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
And Melchom will go into captivity, he and his leaders together, says the Lord.

< Amos 1 >