< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
I min förra skrift, gode Teofilus, har jag berättat om allt vad Jesus gjorde och lärde,
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
ända till den dag då han blev upptagen, sedan han genom helig ande hade givit sina befallningar åt apostlarna som han hade utvalt.
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
För dem hade han ock genom många säkra bevis tett sig såsom levande, efter utståndet lidande; ty under fyrtio dagar lät han sig ses av dem och talade med dem om Guds rike.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
När han då var tillsammans med dem, bjöd han dem och sade: »Lämnen icke Jerusalem, utan förbiden där vad Fadern har utlovat, det varom I haven hört av mig.
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Ty Johannes döpte med vatten, men få dagar härefter skolen I bliva döpta i helig ande.»
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
Då de nu hade kommit tillhopa, frågade de honom och sade: »Herre, skall du nu i denna tid upprätta igen riket åt Israel?»
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
Han svarade dem: »Det tillkommer icke eder att få veta tider eller stunder som Fadern i sin makt har fastställt.
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
Men när den helige Ande kommer över eder, skolen I undfå kraft och bliva mina vittnen, både i Jerusalem och i hela Judeen och Samarien, och sedan intill jordens ända.»
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
När han hade sagt detta, lyftes han inför deras ögon upp i höjden, och en sky tog honom bort ur deras åsyn.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
Och medan de skådade mot himmelen, under det han for upp, se, då stodo hos dem två män i vita kläder.
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
Och dessa sade: »I galileiske män, varför stån I och sen mot himmelen? Denne Jesus, som har blivit upptagen från eder till himmelen, han skall komma igen på samma sätt som I haven sett honom fara upp till himmelen.»
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Sedan vände de tillbaka till Jerusalem från det berg som kallas Oljeberget, vilket ligger nära Jerusalem, icke längre därifrån, än man får färdas på en sabbat.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
Och när de hade kommit dit, gingo de upp i den sal i övre våningen, där de plägade vara tillsammans: Petrus och Johannes och Jakob och Andreas, Filippus och Tomas, Bartolomeus och Matteus, Jakob, Alfeus' son, och Simon ivraren och Judas, Jakobs son.
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
Alla dessa höllo endräktigt ut i bön tillika med Maria, Jesu moder, och några andra kvinnor samt Jesu bröder.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
En av de dagarna stod Petrus upp och talade bland bröderna, som då voro församlade till ett antal av omkring etthundratjugu; han sade:
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
»Mina bröder, det skriftens ord skulle fullbordas, som den helige Ande genom Davids mun hade profetiskt talat om Judas, vilken blev vägvisare åt de män som grepo Jesus.
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
Han var ju räknad bland oss och hade också fått detta ämbete på sin lott.
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
Och med de penningar han hade fått såsom lön för sin ogärning förvärvade han sig en åker. Men han störtade framstupa ned, och hans kropp brast mitt itu, så att alla hans inälvor gåvo sig ut.
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
Detta blev bekant för alla Jerusalems invånare, och så blev den åkern på deras tungomål kallad Akeldamak (det betyder Blodsåkern).
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
Så är ju skrivet i Psalmernas bok: 'Hans gård blive öde, och ingen må finnas, som bor däri'; och vidare: 'Hans ämbete tage en annan.'
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
Därför bör nu någon av de män som följde oss under hela den tid då Herren Jesus gick ut och in bland oss,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
allt ifrån den dag då han döptes av Johannes ända till den dag då han blev upptagen och skildes ifrån oss -- någon av dessa män bör insättas till att jämte oss vittna om hans uppståndelse.»
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
Därefter ställde de fram två: Josef (som kallades Barsabbas och hade tillnamnet Justus) och Mattias.
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
Och de bådo och sade: »Herre, du som känner allas hjärtan, visa oss vilken av dessa två du har utvalt
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
till att få den plats såsom tjänare och apostel, vilken Judas övergav, för att gå till den plats som var hans.»
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
Och de drogo lott om dem, och lotten föll på Mattias. Och så blev denne, jämte de elva, räknad såsom apostel.

< Ayyukan Manzanni 1 >