< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
The former book I wrote, Theophilus, told all that Jesus began to do and to teach,
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
until the day that he was taken up, after he had given commands through the Holy Spirit to the apostles he had chosen.
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
After his suffering, he presented himself alive to them with many convincing proofs. For forty days he appeared to them, and he spoke about the kingdom of God.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
When he was meeting together with them, he commanded them not to leave Jerusalem, but to wait for the promise of the Father, about which, he said, “You heard from me
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
that John indeed baptized with water, but you shall be baptized in the Holy Spirit in a few days.”
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
When they were assembled together they asked him, “Lord, is this the time you will restore the kingdom to Israel?”
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
He said to them, “It is not for you to know the times or the seasons which the Father has determined by his own authority.
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
But you will receive power, when the Holy Spirit comes upon you, and you will be my witnesses both in Jerusalem and in all Judea and Samaria, and to the ends of the earth.”
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
When the Lord Jesus had said these things, as they were looking up, he was raised up, and a cloud hid him from their eyes.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
While they were looking intensely to heaven as he went, suddenly, two men stood by them in white clothing.
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
They said, “You men of Galilee, why do you stand here looking into heaven? This Jesus who has been taken up from you into heaven, will return in the same manner as you saw him going into heaven.”
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Then they returned to Jerusalem from the Mount of Olives, which is near to Jerusalem, a Sabbath day's journey.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
When they arrived, they went up into the upper chamber, where they were staying. They were Peter, John, James, Andrew, Philip, Thomas, Bartholomew, Matthew, James son of Alphaeus, Simon the Zealot, and Judas son of James.
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
They were all united as one, as they diligently continued in prayer. Included were the women, Mary the mother of Jesus, and his brothers.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
In those days Peter stood up in the midst of the brothers, about 120 people, and said,
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
“Brothers, it was necessary that the scripture should be fulfilled, that the Holy Spirit spoke before by the mouth of David concerning Judas, who guided the ones who arrested Jesus.
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
For he was one of us and received his share of the benefits of this ministry.”
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
(Now this man bought a field with the earnings he received for his wickedness, and there he fell headfirst, and his body burst open, and all his intestines poured out.
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
All those living in Jerusalem heard about this, so they called that field in their language “Akeldama,” that is, “Field of Blood.”)
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
“For it is written in the Book of Psalms, 'Let his field be made desolate, and do not let even one person live there'; 'Let someone else take his position of leadership.'
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
It is necessary, therefore, that one of the men who accompanied us all the time the Lord Jesus went in and out among us,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
beginning from the baptism of John to the day that he was taken up from us, must be a witness with us of his resurrection.”
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
They put forward two men, Joseph called Barsabbas, who was also named Justus, and Matthias.
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
They prayed and said, “You, Lord, know the hearts of all people, so reveal which of these two is the one whom you have chosen
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
to take the place in this ministry and apostleship from which Judas turned away to go to his own place.”
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
They cast lots for them, and the lot fell to Matthias, and he was numbered with the eleven apostles.

< Ayyukan Manzanni 1 >