< Ayyukan Manzanni 1 >
1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
The first narrative, indeed, made I, concerning all things, O Theophilus, which Jesus began both to do and teach, —
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
Until the day when, having given command unto the apostles, whom through Holy Spirit he had chosen, he was taken up;
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
Unto whom he also presented himself alive, after he had suffered, by many sure tokens, throughout forty days making himself visible unto them, and speaking the things concerning the kingdom of God.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
And being in company with them he charged them, from Jerusalem, not to absent themselves, but—To abide around the promise of the Father which ye have heard of me,
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Because, John, indeed, immersed with water; but, ye, in Holy Spirit shall be immersed, —after not many of these days.
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
They, therefore, having come together, began to question him, saying—Lord! art thou at this time duly establishing the kingdom unto Israel?
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
He said unto them—It is not yours to get to know times or seasons which the Father hath put in his own authority;
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
But ye shall receive power when the Holy Spirit cometh upon you, and ye shall be my witnesses, both in Jerusalem and [in] all Judaea and Samaria and as far as the uttermost part of the land.
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
And having said these things, as they were beholding, he was lifted up, and a cloud caught him away from their eyes.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
And, while they were looking steadfastly into heaven as he was going his way, then lo! two men had taken their stand beside them, in white garments, —
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
Who also said—Men of Galilee! why stand ye looking into heaven? This Jesus who hath been taken up from you into heaven, shall so come, in like manner as ye yourselves have gazed upon him going into heaven.
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Then returned they into Jerusalem, from a mountain called Olivet, which is nigh unto Jerusalem a Sabbath day’s journey.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
And, when they had entered, into the upper-story went they up, where remained behind—both Peter and John and James and Andrew, Philip and Thomas, Bartholomew and Matthew, James the son of Alphaeus and Simon the zealot, and Judas the son of James.
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
These all were giving constant attention with one accord unto the prayer, with [certain] women, and Mary the mother of Jesus, and with his brethren.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
And, in these days, Peter, standing up in the midst of the brethren, said, —and there was a multitude of names, of one accord, about a hundred and twenty, —
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
Brethren! It was needful for the Scripture to be fulfilled which the Holy Spirit spake beforehand through the mouth of David, concerning Judas, —who became guide unto them who apprehended Jesus;
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
For that he had come to be reckoned among us and obtained the lot of this ministry.—
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
This man therefore had possessed himself of a field out of the reward of unrighteousness, —and falling headlong burst asunder in the midst, and forth gushed all his bowels;
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
And it became known unto all them who were dwelling in Jerusalem, so that that field was called, in their language, Akeldama, that is, Field of Blood.—
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
For it is written in the book of Psalms: Let his encampment become desolate, and let there be none to dwell therein! And—his overseership, let a different man take!
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
It is needful then that, of the men who companied with us during all the time in which the Lord Jesus came in and went out over us,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
Beginning from the immersion by John until the day when he was taken up from us, that, a witness of his resurrection along with us, should one of these become.
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
And they appointed two, —Joseph, called Barsabbas, who was surnamed Justus, and Matthias.
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
And, praying, they said—Thou Lord! observer of the hearts of all men! shew forth whom thou hast chosen, —of these two, one; —
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
To take the place of this ministry and apostleship, from which Judas went aside, to go his way unto his own place.
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
And they gave lots for them; and the lot fell upon Matthias, and he was numbered with the eleven apostles.