< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
The first account I wrote, Theophilus, concerned all that Yeshua began both to do and to teach,
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
until the day in which he was received up, after he had given commandment through the Rukha d'Qudsha to the apostles whom he had chosen.
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
To these he also showed himself alive after he suffered, by many proofs, appearing to them over a period of forty days, and speaking about God's Kingdom.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
Being assembled together with them, he commanded them, "Do not depart from Urishlim, but wait for the promise of the Father, which you heard from me.
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
For Yukhanan indeed baptized in water, but you will be baptized in the Rukha d'Qudsha not many days from now."
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
Therefore, when they had come together, they asked him, "Lord, are you now restoring the kingdom to Israyel?"
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
He said to them, "It is not for you to know times or seasons which the Father has set within his own authority.
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
But you will receive power when the Rukha d'Qudsha has come upon you. You will be my witnesses in Urishlim, in all Yehuda and Samaria, and to the farthest part of the earth."
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
When he had said these things, as they were looking, he was taken up, and a cloud took him out of their sight.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
While they were looking steadfastly into the sky as he went, look, two men stood by them in white clothing,
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
who also said, "You men of Galila, why do you stand looking into the sky? This Yeshua, who was received up from you into the sky will come back in the same way as you saw him going into the sky."
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Then they returned to Urishlim from the mountain called Olivet, which is near Urishlim, a Sabbath day's journey away.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
When they had come in, they went up into the upper room, where they were staying; that is Kipha, Yukhanan, Yaquv, Andreus, Philipus, Tama, Bar-Tulmai, Mattai, Yehudah the son of Khalphai, Shimon the Zealot, and Yehudah the son of Yaquv.
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
All these with one accord continued steadfastly in prayer, along with the women, and Maryam the mother of Yeshua, and with his brothers.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
In these days, Kipha stood up in the midst of the brothers (and the number of names was about one hundred twenty), and said,
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
"Brothers, it was necessary that this Scripture should be fulfilled, which the Rukha d'Qudsha spoke before by the mouth of Dawid concerning Yehudah, who was guide to those who took Yeshua.
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
For he was numbered with us, and received his portion in this ministry.
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
Now this man obtained a field with the reward for his wickedness, and falling headfirst his body burst open, and all his intestines gushed out.
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
It became known to everyone who lived in Urishlim that in their language that field was called 'Khaqel-Dema,' that is, 'The field of blood.'
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
For it is written in the scroll of Psalms, 'Let his habitation be made desolate, and let no one dwell in it;' and, 'Let another take his office.'
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
"Of the men therefore who have accompanied us all the time that the Lord Yeshua went in and out among us,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
beginning from the baptism of Yukhanan, to the day that he was received up from us, of these one must become a witness with us of his resurrection."
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
They put forward two, Yauseph called Bar-Shaba, who was surnamed Justus, and Matiya.
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
They prayed, and said, "You, Lord, who know the hearts of all people, show which one of these two you have chosen
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
to take part in this ministry and office of apostle from which Yehudah turned away to go to his own place."
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
They drew lots for them, and the lot fell on Matya, and he was numbered with the eleven apostles.

< Ayyukan Manzanni 1 >