< Ayyukan Manzanni 9 >

1 Ana cikin haka, Shawulu ya ɗage yana barazana yin kisa da tsananta wa almajiran Ubangiji. Sai ya je wurin babban firist
Now Saul, whose every breath was a threat of destruction for the disciples of the Lord,
2 ya roƙe shi ya ba shi wasiƙu zuwa majami’un Damaskus, don in ya sami wani a wurin wanda yake bin wannan Hanya, ko maza ko mata, yă kama su a matsayin’yan kurkuku yă kai Urushalima.
went to the High Priest and begged from him letters addressed to the synagogues in Damascus, in order that if he found any believers there, either men or women, he might bring them in chains to Jerusalem.
3 Da ya yi kusa da Damaskus a kan hanyarsa, ba zato ba tsammani sai wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi.
But on the journey, as he was getting near Damascus, suddenly there flashed round him a light from Heaven;
4 Sai ya fāɗi a ƙasa ya kuma ji wata murya ta ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”
and falling to the ground he heard a voice which said to him, "Saul, Saul, why are you persecuting Me?"
5 Shawulu ya yi tambaya ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Ya amsa ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
"Who art thou, Lord?" he asked. "I am Jesus, whom you are persecuting," was the reply.
6 Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
"But rise and go to the city, and you will be told what you are to do.
7 Mutanen da suke tafiya tare da Shawulu suka rasa bakin magana; sun ji muryar amma ba su ga kowa ba.
Meanwhile the men who travelled with Saul were standing dumb with amazement, hearing a sound, but seeing no one.
8 Shawulu ya tashi daga ƙasa, amma sa’ad da ya buɗe idanunsa bai iya ganin wani abu ba. Saboda haka aka kama hannunsa aka yi masa jagora zuwa cikin Damaskus.
Then he rose from the ground, but when he had opened his eyes, he could not see, and they led him by the arm and brought him to Damascus.
9 Kwana uku yana a makance, bai ci ba bai kuma sha kome ba.
And for two days he remained without sight, and did not eat or drink anything.
10 A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
Now in Damascus there was a disciple of the name of Ananias. The Lord spoke to him in a vision, saying, "Ananias!" "I am here, Lord," he answered.
11 Ubangiji ya ce masa, “Je gidan Yahuda da yake a Miƙaƙƙen Titi ka yi tambaya ko akwai wani mutum daga Tarshish mai suna Shawulu, gama ga shi yana addu’a.
"Rise," said the Lord, "and go to Straight Street, and inquire at the house of Judas for a man called Saul, from Tarsus, for he is actually praying.
12 Cikin wahayi ya ga wani mutum mai suna Ananiyas ya zo ya sa hannuwansa a kansa don yă sāke samun ganin gari.”
He has seen a man called Ananias come and lay his hands upon him so that he may recover his sight."
13 Ananiyas ya amsa ya ce, “Ubangiji, na ji labarin mutumin nan sosai da kuma duk lahanin da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.
"Lord," answered Ananias, "I have heard about that man from many, and I have heard of the great mischief he has done to Thy people in Jerusalem;
14 Ga shi kuma ya zo nan da izinin manyan firistoci, don yă kama duk wanda yake kiran bisa sunanka.”
and here he is authorized by the High Priests to arrest all who call upon Thy name."
15 Amma Ubangiji ya ce wa Ananiyas, “Je ka! Wannan mutum zaɓaɓɓen kayan aikina ne don yă kai sunana a gaban Al’ummai da sarakunansu da kuma a gaban mutanen Isra’ila.
"Go," replied the Lord; "he is a chosen instrument of Mine to carry My name to the Gentiles and to kings and to the descendants of Israel.
16 Zan nuna masa wahalar da dole zai sha saboda sunana.”
For I will let him know the great sufferings which he must pass through for My sake."
17 Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
So Ananias went and entered the house; and, laying his two hands upon Saul, said, "Saul, brother, the Lord--even Jesus who appeared to you on your journey--has sent me, that you may recover your sight and be filled with the Holy Spirit."
18 Nan da nan, sai wani abu kamar ɓawo ya fāɗo daga idanun Shawulu, ya kuma sāke iya ganin gari. Sai ya tashi aka kuma yi masa baftisma,
Instantly there dropped from his eyes what seemed to be scales, and he could see once more. Upon this he rose and received baptism;
19 bayan ya ci abinci, sai sāke samun ƙarfi. Shawulu ya yi kwanaki masu yawa tare da almajiran da suke a Damaskus.
after which he took food and regained his strength. Then he remained some little time with the disciples in Damascus.
20 Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
And in the synagogues he began at once to proclaim Jesus as the Son of God;
21 Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”
and his hearers were all amazed, and began to ask one another, "Is not this the man who in Jerusalem tried to exterminate those who called upon that Name, and came here on purpose to carry them off in chains to the High Priests?"
22 Duk da haka Shawulu ya yi ta ƙara ƙarfi, ya kuma rikitar da Yahudawan da suke zaune a Damaskus, ta wurin tabbatar musu cewa, Yesu shi ne Kiristi.
Saul, however, gained more and more influence, and as for the Jews living in Damascus, he bewildered them with his proofs that Jesus is the Christ.
23 Bayan kwanaki masu yawa, sai Yahudawa suka haɗa baki su kashe shi,
At length the Jews plotted to kill Saul;
24 amma Shawulu ya sami labarin shirinsu. Dare da rana suka yi fakonsa a ƙofofin birnin don su kashe shi.
but information of their intention was given to him. They even watched the gates, day and night, in order to murder him;
25 Amma almajiransa suka ɗauke shi da dare suka saukar da shi a cikin kwando ta taga a katanga.
but his disciples took him by night and let him down through the wall, lowering him in a hamper.
26 Da ya zo Urushalima, ya yi ƙoƙarin shiga cikin almajiran amma dukansu suka ji tsoronsa, ba su gaskata cewa tabbatacce shi almajiri ba ne.
So he came to Jerusalem and made several attempts to associate with the disciples, but they were all afraid of him, being in doubt as to whether he himself was a disciple.
27 Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
Barnabas, however, came to his assistance. He brought Saul to the Apostles, and related to them how, on his journey, he had seen the Lord, and that the Lord had spoken to him, and how in Damascus he had fearlessly taught in the name of Jesus.
28 Saboda haka Shawulu ya zauna tare da su yana kai da kawowa a sake a cikin Urushalima, yana magana gabagadi a cikin sunan Ubangiji.
Henceforth Saul was one of them, going in and out of the city,
29 Ya yi magana ya kuma yi muhawwara da Yahudawa masu jin Hellenanci, amma suka yi ƙoƙarin kashe shi.
and speaking fearlessly in the name of the Lord. And he often talked with the Hellenists and had discussions with them.
30 Sa’ad da’yan’uwa suka sami labarin wannan, sai suka ɗauke shi zuwa Kaisariya suka aika da shi Tarshish.
But they kept trying to take his life. On learning this, the brethren brought him down to Caesarea, and then sent him by sea to Tarsus.
31 Sa’an nan ikkilisiya ko’ina a Yahudiya, Galili da kuma Samariya ta sami salama. Ta yi ƙarfi; ta kuma ƙarfafa ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ta ƙaru sosai tana rayuwa cikin tsoron Ubangiji.
The Church, however, throughout the whole of Judaea, Galilee and Samaria, had peace and was spiritually built up; and grew in numbers, living in the fear of the Lord and receiving encouragement from the Holy Spirit.
32 Da Bitrus yake zazzaga ƙasar, sai ya je ya ziyarci tsarkakan da suke a Lidda.
Now Peter, as he went to town after town, came down also to God's people at Lud.
33 A can ya tarar da wani mutum mai suna Eniyas, shanyayye wanda yake kwance kan gado shekara takwas.
There he found a man of the name of Aeneas, who for eight years had kept his bed, through being paralysed.
34 Sai Bitrus ya ce masa, “Eniyas, Yesu Kiristi ya warkar da kai. Tashi ka naɗe tabarmarka.” Nan da nan Eniyas ya tashi.
Peter said to him, "Aeneas, Jesus Christ cures you. Rise and make your own bed." He at once rose to his feet.
35 Duk waɗanda suke zama a Lidda da Sharon suka gan shi suka kuma juyo ga Ubangiji.
And all the people of Lud and Sharon saw him; and they turned to the Lord.
36 A Yoffa akwai wata almajira mai suna Tabita (a harshen Girik sunanta shi ne Dokas); ita mai aikin alheri ce kullum, tana kuma taimakon matalauta.
Among the disciples at Jaffa was a woman called Tabitha, or, as the name may be translated, 'Dorcas.' Her life was wholly devoted to the good and charitable actions which she was constantly doing.
37 A lokacin nan ta yi rashin lafiya ta mutu, aka kuma yi wa gawarta wanka aka ajiye a wani ɗaki a gidan sama.
But, as it happened, just at that time she was taken ill and died. After washing her body they laid it out in a room upstairs.
38 Lidda yana kusa da Yoffa; saboda haka sa’ad da almajirai suka ji cewa Bitrus yana a Lidda, sai suka aiki mutum biyu wurinsa su roƙe shi cewa, “In ka yarda ka zo nan da nan!”
Lud, however, being near Jaffa, the disciples, who had heard that Peter was at Lud, sent two men to him with an urgent request that he would come across to them without delay.
39 Sai Bitrus ya tafi tare da su, sa’ad da ya iso sai aka kai shi ɗakin saman. Duka gwauraye suka tsaya kewaye da shi, suna kuka suna nunnuna masa riguna da kuma waɗansu tufafin da Dokas ta yi yayinda take tare da su.
So Peter rose and went with them. On his arrival they took him upstairs, and the widow women all came and stood by his side, weeping and showing him the underclothing and cloaks and garments of all kinds which Dorcas used to make while she was still with them.
40 Bitrus ya fitar da su duka daga ɗakin; sa’an nan ya durƙusa ya yi addu’a. Da ya juya wajen matacciyar, sai ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe idanunta, ta ga Bitrus sai ta tashi zaune.
Peter, however, putting every one out of the room, knelt down and prayed, and then turning to the body, he said, "Tabitha, rise." Dorcas at once opened her eyes, and seeing Peter, sat up.
41 Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.
Then, giving her his hand, he raised her to her feet and, calling to him God's people and the widows, he gave her back to them alive.
42 Wannan ya zama sananne ko’ina a Yoffa, mutane da yawa kuma suka gaskata da Ubangiji.
This incident became known throughout Jaffa, and many believed in the Lord;
43 Bitrus ya zauna a Yoffa na ɗan lokaci tare da wani mai aikin fatu mai suna Siman.
and Peter remained for a considerable time at Jaffa, staying at the house of a man called Simon, a tanner.

< Ayyukan Manzanni 9 >