< Ayyukan Manzanni 9 >

1 Ana cikin haka, Shawulu ya ɗage yana barazana yin kisa da tsananta wa almajiran Ubangiji. Sai ya je wurin babban firist
Meanwhile, Saul angrily continued to say, “I will kill those who believe that [Jesus is] the Lord!” He went to the supreme priest [in Jerusalem]
2 ya roƙe shi ya ba shi wasiƙu zuwa majami’un Damaskus, don in ya sami wani a wurin wanda yake bin wannan Hanya, ko maza ko mata, yă kama su a matsayin’yan kurkuku yă kai Urushalima.
and requested him [to write] letters [introducing him] to [the leaders of] [MTY] the Jewish meeting places in Damascus [city. The letters asked them to authorize Saul] to seize any men or women who followed the way [that Jesus had taught], and to take them as prisoners to Jerusalem [so that the Jewish leaders could judge and punish them].
3 Da ya yi kusa da Damaskus a kan hanyarsa, ba zato ba tsammani sai wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi.
Saul took those letters, and while he [and those with him] traveled toward Damascus, as they were approaching the city, suddenly a [brilliant] light from heaven shone around Saul.
4 Sai ya fāɗi a ƙasa ya kuma ji wata murya ta ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”
[Immediately] he fell down to the ground. Then he heard the voice [of the Lord] say to him, “Saul, Saul, (stop causing me to suffer!/why are you causing me to suffer?) [RHQ]”
5 Shawulu ya yi tambaya ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Ya amsa ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
Saul asked him, “Lord, who are you?” He replied, “I am Jesus, [and] you [(sg)] are causing me to suffer [by hurting my followers]!
6 Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
Now instead [of continuing to do that], stand up and go into the city! [Someone there] will tell you [(sg)] what I [want] you to do.”
7 Mutanen da suke tafiya tare da Shawulu suka rasa bakin magana; sun ji muryar amma ba su ga kowa ba.
The men who were traveling with Saul [became so frightened that they] could not say anything. [They just] stood there. They only heard the sound [when the Lord spoke], but they did not see anyone.
8 Shawulu ya tashi daga ƙasa, amma sa’ad da ya buɗe idanunsa bai iya ganin wani abu ba. Saboda haka aka kama hannunsa aka yi masa jagora zuwa cikin Damaskus.
Saul got up from the ground, but when he opened his eyes he could not see anything. So the men [with him] took him by the hand and led him into Damascus.
9 Kwana uku yana a makance, bai ci ba bai kuma sha kome ba.
For the next three days Saul could not see [anything], and he did not eat or drink anything.
10 A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
In Damascus there was [a Jew] named Ananias who believed in Jesus. While [Ananias was seeing] a vision, the Lord [Jesus] said to him, “Ananias!” He replied, “Lord, I [am listening].”
11 Ubangiji ya ce masa, “Je gidan Yahuda da yake a Miƙaƙƙen Titi ka yi tambaya ko akwai wani mutum daga Tarshish mai suna Shawulu, gama ga shi yana addu’a.
The Lord Jesus told him, “Go to Straight Street to the house that belongs to Judas. Ask [someone there if you(sg) can talk to] a man named Saul from Tarsus [city], because, surprisingly, at this moment he is praying [to me].
12 Cikin wahayi ya ga wani mutum mai suna Ananiyas ya zo ya sa hannuwansa a kansa don yă sāke samun ganin gari.”
[Saul has seen] a vision in which a man named Ananias entered [the house where he was staying] and put his hands on him in order that he might see again.”
13 Ananiyas ya amsa ya ce, “Ubangiji, na ji labarin mutumin nan sosai da kuma duk lahanin da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.
But Ananias [protested], saying, “But Lord, many people have told me about this man! He has done many evil things to the people in Jerusalem who [believe in] you!
14 Ga shi kuma ya zo nan da izinin manyan firistoci, don yă kama duk wanda yake kiran bisa sunanka.”
And the chief priests have authorized him to come here [to Damascus] in order to seize all of us who believe in you [(sg)] [MTY] [and take us to Jerusalem]!”
15 Amma Ubangiji ya ce wa Ananiyas, “Je ka! Wannan mutum zaɓaɓɓen kayan aikina ne don yă kai sunana a gaban Al’ummai da sarakunansu da kuma a gaban mutanen Isra’ila.
But the Lord [Jesus] told Ananias, “Go to [Saul! Do what I say], because I have chosen him to serve me in order that he might speak about me [MTY] both to non-Jewish people and [their] kings and to the Israeli people.
16 Zan nuna masa wahalar da dole zai sha saboda sunana.”
I myself will tell him that he must often suffer greatly because of [telling people about] me [MTY].”
17 Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
So Ananias went, and [after he found] the house [where Saul was], he entered it. Then, [as soon as he met Saul], he put his hands on him, and he said, “Brother Saul, the Lord Jesus [himself] commanded me to come [to you]. He is the [same] one who appeared to you [(sg)] while you were traveling along the road. [He sent me to you] in order that you might see again and that you might be completely controlled by the Holy Spirit {that the Holy Spirit might completely control you}.”
18 Nan da nan, sai wani abu kamar ɓawo ya fāɗo daga idanun Shawulu, ya kuma sāke iya ganin gari. Sai ya tashi aka kuma yi masa baftisma,
Instantly, things like [fish] scales fell from Saul’s eyes, and he was able to see again. Then he stood up and was baptized {[Ananias] baptized him} [immediately].
19 bayan ya ci abinci, sai sāke samun ƙarfi. Shawulu ya yi kwanaki masu yawa tare da almajiran da suke a Damaskus.
After Saul ate some food, he felt strong again. Saul stayed with the [other] believers in Damascus for several days.
20 Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Right away Saul began to preach [to people about Jesus] in the Jewish meeting places [in Damascus. He told them] that Jesus is (the Son of/the man who is also) God.
21 Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”
And all the people who heard him [preach] were amazed. [Various ones of] them were saying, “([We(inc) can hardly believe that] this is the [same man] who persecuted the believers in Jerusalem!/Is this really the [same man] who persecuted the believers in Jerusalem?) [RHQ, MTY] And we [(inc)] know that he has [RHQ] come here to seize us and take us to the chief priests [in Jerusalem]!”
22 Duk da haka Shawulu ya yi ta ƙara ƙarfi, ya kuma rikitar da Yahudawan da suke zaune a Damaskus, ta wurin tabbatar musu cewa, Yesu shi ne Kiristi.
But [God] enabled Saul [to preach to many people even] more convincingly. He was proving [from the Scriptures] that Jesus is the Messiah. So the Jewish leaders in Damascus could not think of anything (to refute [what he said/to prove that what he said was not true]).
23 Bayan kwanaki masu yawa, sai Yahudawa suka haɗa baki su kashe shi,
Some time later, [after Saul had left Damascus and then returned], the Jewish [leaders] [SYN] [there] plotted to kill him.
24 amma Shawulu ya sami labarin shirinsu. Dare da rana suka yi fakonsa a ƙofofin birnin don su kashe shi.
[During each] day and night those Jews were continually watching [the people passing through] the city gates, in order that [when they saw Saul] they might kill him. However, someone told Saul what they planned to do.
25 Amma almajiransa suka ɗauke shi da dare suka saukar da shi a cikin kwando ta taga a katanga.
So some of those whom he had helped [to believe in Jesus] took him [one] night [to the high stone wall that surrounded the city]. They [used ropes to] lower him in a [large] basket through an opening in the wall. [So he escaped from Damascus].
26 Da ya zo Urushalima, ya yi ƙoƙarin shiga cikin almajiran amma dukansu suka ji tsoronsa, ba su gaskata cewa tabbatacce shi almajiri ba ne.
When Saul arrived in Jerusalem, he began trying to associate with other believers. However, [almost] all of them continued to be afraid of him, because they did not believe that he had become a believer.
27 Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
But Barnabas took him and brought him to the apostles. He explained to the apostles how, [while Saul was traveling] along the road [to Damascus], he had seen the Lord [Jesus] and how the Lord had spoken to him [there. He] also told them how Saul had preached boldly about Jesus [MTY] [to people] in Damascus. [The apostles believed Barnabas and told the other believers about that].
28 Saboda haka Shawulu ya zauna tare da su yana kai da kawowa a sake a cikin Urushalima, yana magana gabagadi a cikin sunan Ubangiji.
So Saul began to associate with the apostles [and other believers] throughout Jerusalem, and he spoke boldly [to people] about [MTY] the Lord [Jesus].
29 Ya yi magana ya kuma yi muhawwara da Yahudawa masu jin Hellenanci, amma suka yi ƙoƙarin kashe shi.
Saul was [also] speaking [about Jesus] with Jews who spoke Greek, and he was debating with them. But they were continually trying [to think] ([of a way] to kill him/of [how they could] kill him).
30 Sa’ad da’yan’uwa suka sami labarin wannan, sai suka ɗauke shi zuwa Kaisariya suka aika da shi Tarshish.
When the [other] believers heard that [those Jews were planning to kill him, some of] the believers took Saul down to Caesarea [city. There] they arranged for him to go [by ship] to Tarsus, [his hometown].
31 Sa’an nan ikkilisiya ko’ina a Yahudiya, Galili da kuma Samariya ta sami salama. Ta yi ƙarfi; ta kuma ƙarfafa ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ta ƙaru sosai tana rayuwa cikin tsoron Ubangiji.
So the groups of believers throughout [the entire regions of] Judea, Galilee, and Samaria lived peacefully [because no one was persecuting them any more]. The Holy Spirit was strengthening them [spiritually] and encouraging them. They were continuing to revere/honor the Lord [Jesus, and the Holy Spirit] was enabling many other people [to become believers].
32 Da Bitrus yake zazzaga ƙasar, sai ya je ya ziyarci tsarkakan da suke a Lidda.
While Peter was traveling throughout those [regions, once] he went to [the coastal plain to visit] the believers [who lived] in Lydda [town].
33 A can ya tarar da wani mutum mai suna Eniyas, shanyayye wanda yake kwance kan gado shekara takwas.
There he met a man whose name was Aeneas. Aeneas had not been able to get up from [his] bed for eight years, because he was paralyzed.
34 Sai Bitrus ya ce masa, “Eniyas, Yesu Kiristi ya warkar da kai. Tashi ka naɗe tabarmarka.” Nan da nan Eniyas ya tashi.
Peter said to him, “Aeneas, Jesus Christ heals you [(sg) right now]! Get up and roll up your mat!” Right away Aeneas stood up.
35 Duk waɗanda suke zama a Lidda da Sharon suka gan shi suka kuma juyo ga Ubangiji.
Most of the people who lived in Lydda and on Sharon [Plain] saw Aeneas [after the Lord had healed him], so they believed in the Lord [Jesus].
36 A Yoffa akwai wata almajira mai suna Tabita (a harshen Girik sunanta shi ne Dokas); ita mai aikin alheri ce kullum, tana kuma taimakon matalauta.
In Joppa [town] there was a believer whose name was Tabitha. [Her name] in the [Greek] language was Dorcas. [Both of these names mean gazelle/deer/antelope]. That woman was continually doing good deeds [for others. Specifically], she was helping poor people [by giving them things that they needed].
37 A lokacin nan ta yi rashin lafiya ta mutu, aka kuma yi wa gawarta wanka aka ajiye a wani ɗaki a gidan sama.
During the time [that Peter was in Lydda], she became sick and died. [Some women there] washed her body [according to the Jewish custom so that the people could bury it]. Then they [covered her body with cloth and] placed it in an upstairs room [in her house].
38 Lidda yana kusa da Yoffa; saboda haka sa’ad da almajirai suka ji cewa Bitrus yana a Lidda, sai suka aiki mutum biyu wurinsa su roƙe shi cewa, “In ka yarda ka zo nan da nan!”
Lydda was near Joppa, so when the believers heard that Peter was [still] in Lydda, they sent two men to [go] to Peter. [When they arrived where Peter was], they repeatedly urged/begged him, “Please come immediately with us [to Joppa]!”
39 Sai Bitrus ya tafi tare da su, sa’ad da ya iso sai aka kai shi ɗakin saman. Duka gwauraye suka tsaya kewaye da shi, suna kuka suna nunnuna masa riguna da kuma waɗansu tufafin da Dokas ta yi yayinda take tare da su.
So [right away] Peter got ready and went with them. When they arrived [at the house in Joppa], the two men took Peter to the upstairs room [where Dorcas’ body was lying]. All the widows [there] around Peter. They were crying and showing him the cloaks and [other] garments that Dorcas had made for people while she was still alive.
40 Bitrus ya fitar da su duka daga ɗakin; sa’an nan ya durƙusa ya yi addu’a. Da ya juya wajen matacciyar, sai ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe idanunta, ta ga Bitrus sai ta tashi zaune.
But Peter sent them all out of the room. Then he got down on his knees and prayed. Then, turning toward Tabitha’s body, he said, “Tabitha, stand up!” [Immediately] she opened her eyes and, when she saw Peter, she sat up.
41 Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.
He grasped one of her hands and helped her to stand up. After he had summoned the believers and [especially] the widows [among them to come back in], he showed them that Tabitha was alive [again].
42 Wannan ya zama sananne ko’ina a Yoffa, mutane da yawa kuma suka gaskata da Ubangiji.
[Soon] people everywhere in Joppa knew about that miracle, and as a result many people believed in the Lord [Jesus].
43 Bitrus ya zauna a Yoffa na ɗan lokaci tare da wani mai aikin fatu mai suna Siman.
Peter stayed in Joppa many days with a man named Simon who made leather [from animal skins].

< Ayyukan Manzanni 9 >