< Ayyukan Manzanni 9 >

1 Ana cikin haka, Shawulu ya ɗage yana barazana yin kisa da tsananta wa almajiran Ubangiji. Sai ya je wurin babban firist
Meanwhile Saul, still breathing out threats and murder against the disciples of the Lord, went to the high priest
2 ya roƙe shi ya ba shi wasiƙu zuwa majami’un Damaskus, don in ya sami wani a wurin wanda yake bin wannan Hanya, ko maza ko mata, yă kama su a matsayin’yan kurkuku yă kai Urushalima.
and asked for letters from him to the synagogues in Damascus, so that if he found any who belonged to the Way, whether men or women, he might bring them to Jerusalem as prisoners.
3 Da ya yi kusa da Damaskus a kan hanyarsa, ba zato ba tsammani sai wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi.
As he was going along, he drew near to Damascus, and suddenly a light from heaven flashed around him.
4 Sai ya fāɗi a ƙasa ya kuma ji wata murya ta ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”
Falling to the ground, he heard a voice saying to him, “Saul, Saul, why are yoʋ persecuting me?”
5 Shawulu ya yi tambaya ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Ya amsa ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
Saul said, “Who are yoʋ, Lord?” The Lord said, “I am Jesus, whom yoʋ are persecuting.
6 Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
But rise and enter the city, and yoʋ will be told what yoʋ must do.”
7 Mutanen da suke tafiya tare da Shawulu suka rasa bakin magana; sun ji muryar amma ba su ga kowa ba.
The men who were traveling with Saul stood speechless, hearing the voice but seeing no one.
8 Shawulu ya tashi daga ƙasa, amma sa’ad da ya buɗe idanunsa bai iya ganin wani abu ba. Saboda haka aka kama hannunsa aka yi masa jagora zuwa cikin Damaskus.
Saul rose from the ground, and although his eyes were open, he saw no one. So they led him by the hand and brought him to Damascus.
9 Kwana uku yana a makance, bai ci ba bai kuma sha kome ba.
He went three days without seeing, and neither ate nor drank.
10 A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
Now there was a disciple in Damascus named Ananias. The Lord said to him in a vision, “Ananias.” He said, “Behold, here I am, Lord.”
11 Ubangiji ya ce masa, “Je gidan Yahuda da yake a Miƙaƙƙen Titi ka yi tambaya ko akwai wani mutum daga Tarshish mai suna Shawulu, gama ga shi yana addu’a.
Then the Lord said to him, “Get up and go to the street called Straight, and at the house of Judas look for a man of Tarsus named Saul. For behold, he is praying,
12 Cikin wahayi ya ga wani mutum mai suna Ananiyas ya zo ya sa hannuwansa a kansa don yă sāke samun ganin gari.”
and in a vision he has seen a man named Ananias coming in and laying his hand on him so that he might receive his sight.”
13 Ananiyas ya amsa ya ce, “Ubangiji, na ji labarin mutumin nan sosai da kuma duk lahanin da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.
But Ananias answered, “Lord, I have heard from many about how much evil this man has done to yoʋr saints in Jerusalem.
14 Ga shi kuma ya zo nan da izinin manyan firistoci, don yă kama duk wanda yake kiran bisa sunanka.”
And here he has authority from the chief priests to arrest all who call upon yoʋr name.”
15 Amma Ubangiji ya ce wa Ananiyas, “Je ka! Wannan mutum zaɓaɓɓen kayan aikina ne don yă kai sunana a gaban Al’ummai da sarakunansu da kuma a gaban mutanen Isra’ila.
But the Lord said to him, “Go, for he is a vessel chosen by me to bring my name before Gentiles, kings, and the sons of Israel.
16 Zan nuna masa wahalar da dole zai sha saboda sunana.”
I will show him how much he must suffer for my name's sake.”
17 Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
So Ananias went and entered the house. Laying his hands on Saul, he said, “Brother Saul, the Lord, who appeared to yoʋ on the road by which yoʋ came, has sent me so that yoʋ may receive yoʋr sight and be filled with the Holy Spirit.”
18 Nan da nan, sai wani abu kamar ɓawo ya fāɗo daga idanun Shawulu, ya kuma sāke iya ganin gari. Sai ya tashi aka kuma yi masa baftisma,
Immediately something like scales fell from Saul's eyes, and he received his sight. Then he rose and was baptized,
19 bayan ya ci abinci, sai sāke samun ƙarfi. Shawulu ya yi kwanaki masu yawa tare da almajiran da suke a Damaskus.
and after taking some food, he was strengthened. For several days Saul was with the disciples in Damascus.
20 Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Immediately he began preaching in the synagogues that the Christ is the Son of God.
21 Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”
All who heard it were amazed and said, “Is this not the man who in Jerusalem tried to destroy those who call upon this name, and has he not come here for the purpose of bringing them as prisoners to the chief priests?”
22 Duk da haka Shawulu ya yi ta ƙara ƙarfi, ya kuma rikitar da Yahudawan da suke zaune a Damaskus, ta wurin tabbatar musu cewa, Yesu shi ne Kiristi.
But Saul grew stronger and kept confounding the Jews who dwelt in Damascus, proving that this man Jesus is the Christ.
23 Bayan kwanaki masu yawa, sai Yahudawa suka haɗa baki su kashe shi,
When many days had past, the Jews took counsel together to kill him,
24 amma Shawulu ya sami labarin shirinsu. Dare da rana suka yi fakonsa a ƙofofin birnin don su kashe shi.
but their plot became known to Saul. They started watching the gates both day and night so that they might kill him.
25 Amma almajiransa suka ɗauke shi da dare suka saukar da shi a cikin kwando ta taga a katanga.
But the disciples took him by night and let him down through a window in the city wall, lowering him in a basket.
26 Da ya zo Urushalima, ya yi ƙoƙarin shiga cikin almajiran amma dukansu suka ji tsoronsa, ba su gaskata cewa tabbatacce shi almajiri ba ne.
When Saul arrived in Jerusalem, he tried to join the disciples, but they were all afraid of him because they did not believe that he was a disciple.
27 Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
Barnabas, however, took him and brought him to the apostles. He related to them how Saul had seen the Lord on the road and that the Lord had spoken to him, and how he had been preaching boldly in Damascus in the name of Jesus.
28 Saboda haka Shawulu ya zauna tare da su yana kai da kawowa a sake a cikin Urushalima, yana magana gabagadi a cikin sunan Ubangiji.
So Saul stayed with them and would go into Jerusalem and speak boldly in the name of the Lord Jesus.
29 Ya yi magana ya kuma yi muhawwara da Yahudawa masu jin Hellenanci, amma suka yi ƙoƙarin kashe shi.
He would also speak and debate with the Hellenists, but they were trying to kill him.
30 Sa’ad da’yan’uwa suka sami labarin wannan, sai suka ɗauke shi zuwa Kaisariya suka aika da shi Tarshish.
When the brothers found out about it, they brought him down to Caesarea and sent him off to Tarsus.
31 Sa’an nan ikkilisiya ko’ina a Yahudiya, Galili da kuma Samariya ta sami salama. Ta yi ƙarfi; ta kuma ƙarfafa ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ta ƙaru sosai tana rayuwa cikin tsoron Ubangiji.
So the churches throughout all Judea, Galilee, and Samaria had peace and were being strengthened. Continuing in the fear of the Lord and in the encouragement of the Holy Spirit, they were being multiplied.
32 Da Bitrus yake zazzaga ƙasar, sai ya je ya ziyarci tsarkakan da suke a Lidda.
Now as Peter was traveling from place to place, he went down to the saints who dwelt in Lydda.
33 A can ya tarar da wani mutum mai suna Eniyas, shanyayye wanda yake kwance kan gado shekara takwas.
There he found a man named Aeneas, who was paralyzed and had been confined to a mat for eight years.
34 Sai Bitrus ya ce masa, “Eniyas, Yesu Kiristi ya warkar da kai. Tashi ka naɗe tabarmarka.” Nan da nan Eniyas ya tashi.
Peter said to him, “Aeneas, Jesus Christ has now healed yoʋ; rise and roll up yoʋr mat.” Immediately he rose,
35 Duk waɗanda suke zama a Lidda da Sharon suka gan shi suka kuma juyo ga Ubangiji.
and all who dwelt in Lydda and Sharon saw him and turned to the Lord.
36 A Yoffa akwai wata almajira mai suna Tabita (a harshen Girik sunanta shi ne Dokas); ita mai aikin alheri ce kullum, tana kuma taimakon matalauta.
Now in Joppa there was a disciple named Tabitha (which means “Dorcas”). She was always doing good works and charitable acts.
37 A lokacin nan ta yi rashin lafiya ta mutu, aka kuma yi wa gawarta wanka aka ajiye a wani ɗaki a gidan sama.
In those days she became sick and died, so they washed her body and laid it in an upper room.
38 Lidda yana kusa da Yoffa; saboda haka sa’ad da almajirai suka ji cewa Bitrus yana a Lidda, sai suka aiki mutum biyu wurinsa su roƙe shi cewa, “In ka yarda ka zo nan da nan!”
Lydda was near Joppa, so when the disciples heard that Peter was there, they sent for him, urging him not to delay in coming to them.
39 Sai Bitrus ya tafi tare da su, sa’ad da ya iso sai aka kai shi ɗakin saman. Duka gwauraye suka tsaya kewaye da shi, suna kuka suna nunnuna masa riguna da kuma waɗansu tufafin da Dokas ta yi yayinda take tare da su.
So Peter rose and went with them. When he arrived, they brought him to the upper room, and all the widows stood before him, weeping and showing him all the tunics and cloaks that Dorcas had made while she was still with them.
40 Bitrus ya fitar da su duka daga ɗakin; sa’an nan ya durƙusa ya yi addu’a. Da ya juya wajen matacciyar, sai ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe idanunta, ta ga Bitrus sai ta tashi zaune.
But Peter sent them all outside, knelt down, and prayed. Turning toward the body, he said, “Tabitha, arise.” Then she opened her eyes, and seeing Peter, she sat up.
41 Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.
He gave her his hand and raised her up. Then he called in the saints and the widows and presented her alive.
42 Wannan ya zama sananne ko’ina a Yoffa, mutane da yawa kuma suka gaskata da Ubangiji.
This became known throughout all Joppa, and many believed in the Lord.
43 Bitrus ya zauna a Yoffa na ɗan lokaci tare da wani mai aikin fatu mai suna Siman.
And Peter remained in Joppa for many days with a tanner named Simon.

< Ayyukan Manzanni 9 >