< Ayyukan Manzanni 9 >

1 Ana cikin haka, Shawulu ya ɗage yana barazana yin kisa da tsananta wa almajiran Ubangiji. Sai ya je wurin babban firist
And Saul was still full of threats and deadly hatred against the disciples of our Lord.
2 ya roƙe shi ya ba shi wasiƙu zuwa majami’un Damaskus, don in ya sami wani a wurin wanda yake bin wannan Hanya, ko maza ko mata, yă kama su a matsayin’yan kurkuku yă kai Urushalima.
And he requested that a letter from the high priest might be given him unto Damascus to the synagogues; that if he should find persons pursuing this course, men or women, he might bind and bring them to Jerusalem.
3 Da ya yi kusa da Damaskus a kan hanyarsa, ba zato ba tsammani sai wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi.
And as he was going, and began to approach Damascus, suddenly there was poured upon him a light from heaven.
4 Sai ya fāɗi a ƙasa ya kuma ji wata murya ta ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”
And he fell to the ground; and he heard a voice which said to him: Saul! Saul! why persecutest thou me? It will be hard for thee to kick against the goads.
5 Shawulu ya yi tambaya ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Ya amsa ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
He replied, and said: Who art thou, my Lord? And our Lord said: I am Jesus the Nazarean, whom thou persecutest.
6 Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
But arise and go into the city, and there it will be told thee what thou oughtest to do.
7 Mutanen da suke tafiya tare da Shawulu suka rasa bakin magana; sun ji muryar amma ba su ga kowa ba.
And the men who travelled with him in the way, stood amazed; for they heard merely the voice, and no one was visible to them.
8 Shawulu ya tashi daga ƙasa, amma sa’ad da ya buɗe idanunsa bai iya ganin wani abu ba. Saboda haka aka kama hannunsa aka yi masa jagora zuwa cikin Damaskus.
And Saul arose from the ground; and nothing was visible to him, with his eyes opened. And they took him by the hand, and led him into Damascus.
9 Kwana uku yana a makance, bai ci ba bai kuma sha kome ba.
And he had no sight for three days; and he neither ate nor drank.
10 A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
And there was in Damascus a certain disciple, whose name was Ananias. And the Lord said to him, in a vision: Ananias! And he said: Lo, I am here, my Lord.
11 Ubangiji ya ce masa, “Je gidan Yahuda da yake a Miƙaƙƙen Titi ka yi tambaya ko akwai wani mutum daga Tarshish mai suna Shawulu, gama ga shi yana addu’a.
And our Lord said to him: Arise, go to the street which is called Straight; and inquire in the house of Judas, for Saul who is from the city of Tarsus: for, lo, while he prayed,
12 Cikin wahayi ya ga wani mutum mai suna Ananiyas ya zo ya sa hannuwansa a kansa don yă sāke samun ganin gari.”
he saw in vision a man named Ananias, who came and laid his hand upon him, that his eyes might be opened.
13 Ananiyas ya amsa ya ce, “Ubangiji, na ji labarin mutumin nan sosai da kuma duk lahanin da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.
And Ananias said: My Lord, I have heard of this man, from many, how much evil he hath perpetrated towards thy saints at Jerusalem.
14 Ga shi kuma ya zo nan da izinin manyan firistoci, don yă kama duk wanda yake kiran bisa sunanka.”
And, lo, here also, he hath authority from the chief priests, to bind all them that call on thy name.
15 Amma Ubangiji ya ce wa Ananiyas, “Je ka! Wannan mutum zaɓaɓɓen kayan aikina ne don yă kai sunana a gaban Al’ummai da sarakunansu da kuma a gaban mutanen Isra’ila.
The Lord said to him: Arise and go; for he is to me a chosen vessel, to carry my name to the Gentiles, and to kings, and among the sons of Israel.
16 Zan nuna masa wahalar da dole zai sha saboda sunana.”
For I will show him, how much he is to suffer on account of my name.
17 Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
Then Ananias went to the house to him; and he laid his hand upon him, and said to him: Saul, my brother, our Lord Jesus, he who appeared to thee by the way as thou camest, hath sent me, that thy eyes might be opened, and thou be filled with the Holy Spirit.
18 Nan da nan, sai wani abu kamar ɓawo ya fāɗo daga idanun Shawulu, ya kuma sāke iya ganin gari. Sai ya tashi aka kuma yi masa baftisma,
And immediately there fell from his eyes something like a scab; and his eyes were opened. And he arose and was baptized.
19 bayan ya ci abinci, sai sāke samun ƙarfi. Shawulu ya yi kwanaki masu yawa tare da almajiran da suke a Damaskus.
And he took food, and was invigorated. And he was some days with the disciples of Damascus.
20 Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
And forthwith he announced Jesus, in the synagogues of the Jews, that he is the Son of God.
21 Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”
And all they that heard him were amazed; and they said: Is not this he, who persecuted all them that call on this name in Jerusalem? And lo, for this very thing also, was he sent hither, that he might bind and carry them to the chief priests.
22 Duk da haka Shawulu ya yi ta ƙara ƙarfi, ya kuma rikitar da Yahudawan da suke zaune a Damaskus, ta wurin tabbatar musu cewa, Yesu shi ne Kiristi.
But Saul was the more strengthened; and he confounded those Jews who dwelt at Damascus, while be demonstrated that this is the Messiah.
23 Bayan kwanaki masu yawa, sai Yahudawa suka haɗa baki su kashe shi,
And when he had been there many days, the Jews formed a conspiracy against him, to kill him.
24 amma Shawulu ya sami labarin shirinsu. Dare da rana suka yi fakonsa a ƙofofin birnin don su kashe shi.
And the plot which they sought to execute upon him, was made known to Saul: and they watched the gates of the city by day and by night, in order to kill him.
25 Amma almajiransa suka ɗauke shi da dare suka saukar da shi a cikin kwando ta taga a katanga.
Then the disciples placed him in a basket, and let him down from the wall by night.
26 Da ya zo Urushalima, ya yi ƙoƙarin shiga cikin almajiran amma dukansu suka ji tsoronsa, ba su gaskata cewa tabbatacce shi almajiri ba ne.
And he went to Jerusalem; and he wished to join himself with the disciples, but they were all afraid of him, and did not believe that he was a disciple.
27 Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
But Barnabas took him, and brought him to the legates, and related to them how the Lord appeared to him in the way, and how he conversed with him; and how, in Damascus, he had discoursed openly in the name of Jesus.
28 Saboda haka Shawulu ya zauna tare da su yana kai da kawowa a sake a cikin Urushalima, yana magana gabagadi a cikin sunan Ubangiji.
And he went in and out with them, at Jerusalem.
29 Ya yi magana ya kuma yi muhawwara da Yahudawa masu jin Hellenanci, amma suka yi ƙoƙarin kashe shi.
And he spoke openly in the name of Jesus and disputed with those Jews who understood Greek. But they wished to kill him:
30 Sa’ad da’yan’uwa suka sami labarin wannan, sai suka ɗauke shi zuwa Kaisariya suka aika da shi Tarshish.
and when the brethren knew it, they conducted him by night to Caesarea, and from there they sent him to Tarsus.
31 Sa’an nan ikkilisiya ko’ina a Yahudiya, Galili da kuma Samariya ta sami salama. Ta yi ƙarfi; ta kuma ƙarfafa ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ta ƙaru sosai tana rayuwa cikin tsoron Ubangiji.
Moreover the church, in all Judaea, and in Galilee, and in Samaria, had peace and was edified; and it walked in the fear of God, and abounded in the consolation of the Holy Spirit.
32 Da Bitrus yake zazzaga ƙasar, sai ya je ya ziyarci tsarkakan da suke a Lidda.
And it occurred, that, as Simon travelled about the cities, he came down to the saints also who dwelt in the city of Lydda.
33 A can ya tarar da wani mutum mai suna Eniyas, shanyayye wanda yake kwance kan gado shekara takwas.
And he found a certain man whose name was 'neas, who had lain on a bed and been paralytic eight years.
34 Sai Bitrus ya ce masa, “Eniyas, Yesu Kiristi ya warkar da kai. Tashi ka naɗe tabarmarka.” Nan da nan Eniyas ya tashi.
And Simon said to him: 'neas, Jesus the Messiah doth heal thee; arise, and spread thy bed. And he rose up immediately.
35 Duk waɗanda suke zama a Lidda da Sharon suka gan shi suka kuma juyo ga Ubangiji.
And all they that dwelt at Lydda and Saron, saw him; and they turned to God.
36 A Yoffa akwai wata almajira mai suna Tabita (a harshen Girik sunanta shi ne Dokas); ita mai aikin alheri ce kullum, tana kuma taimakon matalauta.
And there was in the city of Joppa, a certain female disciple named Tabitha; and she was rich in good works, and in the alms which she did.
37 A lokacin nan ta yi rashin lafiya ta mutu, aka kuma yi wa gawarta wanka aka ajiye a wani ɗaki a gidan sama.
And she fell sick in those days, and died; and they washed her, and laid her in an upper room.
38 Lidda yana kusa da Yoffa; saboda haka sa’ad da almajirai suka ji cewa Bitrus yana a Lidda, sai suka aiki mutum biyu wurinsa su roƙe shi cewa, “In ka yarda ka zo nan da nan!”
And the disciples heard that Simon was in the city of Lydda, which is near to Joppa; and they sent two men to him, to request of him that he would not delay to come to them.
39 Sai Bitrus ya tafi tare da su, sa’ad da ya iso sai aka kai shi ɗakin saman. Duka gwauraye suka tsaya kewaye da shi, suna kuka suna nunnuna masa riguna da kuma waɗansu tufafin da Dokas ta yi yayinda take tare da su.
And Simon arose and went with them. And when he arrived, they conducted him to the chamber; and there were assembled around her all the widows, weeping, and showing him the tunics and the cloaks which Tabitha had given them when alive.
40 Bitrus ya fitar da su duka daga ɗakin; sa’an nan ya durƙusa ya yi addu’a. Da ya juya wajen matacciyar, sai ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe idanunta, ta ga Bitrus sai ta tashi zaune.
And Simon put all the people out, and fell on his knees and prayed; and he turned to the corpse and said: Tabitha, arise. And she opened her eyes; and when she saw Simon, she sat up.
41 Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.
And he reached to her his hand, and raised her up: and he called the saints and the widows, and presented her to them alive.
42 Wannan ya zama sananne ko’ina a Yoffa, mutane da yawa kuma suka gaskata da Ubangiji.
And this became known throughout the city; and many believed on our Lord.
43 Bitrus ya zauna a Yoffa na ɗan lokaci tare da wani mai aikin fatu mai suna Siman.
And he tarried in Joppa not a few days: and he lodged in the house of Simon a tanner.

< Ayyukan Manzanni 9 >