< Ayyukan Manzanni 9 >

1 Ana cikin haka, Shawulu ya ɗage yana barazana yin kisa da tsananta wa almajiran Ubangiji. Sai ya je wurin babban firist
YA si Saulo, sisigueja di jumagong juyong y amenaso yan matadura contra y disipulon y Señot, ya mapos para y magas mamale,
2 ya roƙe shi ya ba shi wasiƙu zuwa majami’un Damaskus, don in ya sami wani a wurin wanda yake bin wannan Hanya, ko maza ko mata, yă kama su a matsayin’yan kurkuku yă kai Urushalima.
Ya jagagao catta, para Damasco gui sinagoga, para yaguin jasoda jaye güine na Jinanaoña, masqueseaja, laje pat palaoan, siña ucone preso para Jerusalem.
3 Da ya yi kusa da Damaskus a kan hanyarsa, ba zato ba tsammani sai wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi.
Ya y jinanaoña, susede na matogüe jijot Damasco; ya enseguidas manina gui oriyaña y candet guinen y langet;
4 Sai ya fāɗi a ƙasa ya kuma ji wata murya ta ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?”
Ya podonggüe gui jilo oda, ya jajungog y inagang na ilegña nu güiya: Saulo, Saulo, sa jafa na unpetsisiguejayo?
5 Shawulu ya yi tambaya ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Ya amsa ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
Ya ilegña: Jaye jao Señot? ya ilegña: Guajo si Jesus ni y unpetsisigue:
6 Yanzu ka tashi ka shiga cikin birnin, za a kuma gaya maka abin da dole za ka yi.”
Lao cajulo ya janao falag y siuda, ya ayonae unmasangane jafa unfatinas.
7 Mutanen da suke tafiya tare da Shawulu suka rasa bakin magana; sun ji muryar amma ba su ga kowa ba.
Ya y taotao sija ni y mangachochongña manojgue ya taya cuentosñija; jajujungogja y inagang, lao taya taotao liniiñija.
8 Shawulu ya tashi daga ƙasa, amma sa’ad da ya buɗe idanunsa bai iya ganin wani abu ba. Saboda haka aka kama hannunsa aka yi masa jagora zuwa cikin Damaskus.
Ya si Saulo cajulo guinin y jilo oda; ya anae mababa y atadogña taya jalie, lao mamantiene canaeña, ya macone guato Damasco.
9 Kwana uku yana a makance, bai ci ba bai kuma sha kome ba.
Ya sumaga güije tres na jaane, ni manatan, yan ni chumocho, yan ni gumimen.
10 A Damaskus kuwa akwai wani almajiri mai suna Ananiyas. Ubangiji ya kira shi a cikin wahayi ya ce, “Ananiyas!” Ananiyas ya amsa, “Ga ni, ya Ubangiji.”
Ya estaba güije un disipulo guiya Damasco, na y naanña si Ananias; sa güiya sinangane ni y Señot gui vision, ilegña: Ananias; ya güiya ilegña: Estagüiyajayo Señot.
11 Ubangiji ya ce masa, “Je gidan Yahuda da yake a Miƙaƙƙen Titi ka yi tambaya ko akwai wani mutum daga Tarshish mai suna Shawulu, gama ga shi yana addu’a.
Ya y Señot ilegña nu güiya: Cajulo ya janao falag y caye ni y mafanaan tunas, ya unaligao y guima Judas, uno na y naanña Saulo, taotao Tarso, sa estagüe na mananaetae,
12 Cikin wahayi ya ga wani mutum mai suna Ananiyas ya zo ya sa hannuwansa a kansa don yă sāke samun ganin gari.”
Ya guinin jalie gui vision un taotao na y naanña si Ananias, na mato ya japolo y canaeña guiya güiya para uninafanlie.
13 Ananiyas ya amsa ya ce, “Ubangiji, na ji labarin mutumin nan sosai da kuma duk lahanin da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima.
Ya si Ananias, manope ilegña: Señot, megae jujungog ni este na taotao, na megae na taelaye finatinasña gui mañantosmo guiya Jerusalem.
14 Ga shi kuma ya zo nan da izinin manyan firistoci, don yă kama duk wanda yake kiran bisa sunanka.”
Ya güine na gaeninasiña guinin y magas mamale, para ugode todo ayo sija y umaagang y naanmo.
15 Amma Ubangiji ya ce wa Ananiyas, “Je ka! Wannan mutum zaɓaɓɓen kayan aikina ne don yă kai sunana a gaban Al’ummai da sarakunansu da kuma a gaban mutanen Isra’ila.
Lao y Señot ilegña nu güiya: Janao unjanao; sa güiya y inayeg na nayan guiya guajo, para uchule y naanjo gui menan y Gentiles, yan y ray sija, yan y famaguon Israel:
16 Zan nuna masa wahalar da dole zai sha saboda sunana.”
Sa guajo fumanue güe cuanto mandangculon güinaja, na janesesita umasapet pot y naanjo.
17 Sa’an nan Ananiyas ya tafi gidan ya kuma shiga ciki. Da ya sa hannuwansa a kan Shawulu, sai ya ce, “Ɗan’uwana Shawulu, Ubangiji, Yesu, wanda ya bayyana gare ka a kan hanya yayinda kake zuwa nan, ya aiko ni domin ka sāke gani a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.”
Ya si Ananias jumanao, ya jumalom gui guima; ya japolo y canaeña guiya güiya, ilegña: Chelujo Saulo, y Señot as Jesus ni y mato guiya jago gui chalan anae mamamaela jao, jatagoyo para usiña unlie, yan unbula ni y Espiritu Santo.
18 Nan da nan, sai wani abu kamar ɓawo ya fāɗo daga idanun Shawulu, ya kuma sāke iya ganin gari. Sai ya tashi aka kuma yi masa baftisma,
Ya enseguidas manbasnag guinin y mataña taegüije y guenaf sija: ya manlie, ya cajulo ya matagpange.
19 bayan ya ci abinci, sai sāke samun ƙarfi. Shawulu ya yi kwanaki masu yawa tare da almajiran da suke a Damaskus.
Ya anae chumocho ninametgot. Ya si Saulo güije sija na jaane dumisipulo guiya Damasco.
20 Nan take ya fara wa’azi cikin majami’u cewa Yesu Ɗan Allah ne.
Ya enseguidas japredica gui sinagoga na si Jesus güiya y Lajin Yuus.
21 Dukan waɗanda suka ji shi suka yi mamaki suka ce, “Ba shi ne mutumin da ya tā-da-na-zaune-tsaye a kan masu kira bisa ga wannan sunan a Urushalima ba? Ba ya zo nan ne don yă kai su a matsayin’yan kurkuku ga manyan firistoci ba?”
Lao todo y jumungog güe, ninafanmanman ya ilegñija: Ada ti este ayo y yumulang ayo sija y umagang este na naan guiya Jerusalem? ya guinin mato güine pot enao na jinaso, para ucone ya ugode guato gui magas mamale.
22 Duk da haka Shawulu ya yi ta ƙara ƙarfi, ya kuma rikitar da Yahudawan da suke zaune a Damaskus, ta wurin tabbatar musu cewa, Yesu shi ne Kiristi.
Lao si Saulo lumalametgotja, yan janafangadon y Judio sija ni y mañasaga Damasco, sa jafanue na este si Cristo.
23 Bayan kwanaki masu yawa, sai Yahudawa suka haɗa baki su kashe shi,
Ya anae manmalofan megae na jaane, mandaña y Judio sija para umapuno güe.
24 amma Shawulu ya sami labarin shirinsu. Dare da rana suka yi fakonsa a ƙofofin birnin don su kashe shi.
Lao y ninanggañiñija, matungo gui as Saulo. Ya sija japupulanja y trangcasija, jaane yan puenge para umaquepuno güi.
25 Amma almajiransa suka ɗauke shi da dare suka saukar da shi a cikin kwando ta taga a katanga.
Ayonae macone puenge ni y disipulo, ya masajguane gui un canastra, ya manatunog gui quelat.
26 Da ya zo Urushalima, ya yi ƙoƙarin shiga cikin almajiran amma dukansu suka ji tsoronsa, ba su gaskata cewa tabbatacce shi almajiri ba ne.
Ya anae mato güe Jerusalem, malago na udañae y disipulo sija; lao sija manmaañao nu güiya, ya ti majonggue na disipulo güe.
27 Amma Barnabas ya ɗauke shi ya kawo shi wurin manzanni. Ya gaya musu yadda Shawulu a kan hanyarsa ya ga Ubangiji kuma cewa Ubangiji ya yi magana da shi, da yadda a Damaskus ya yi wa’azi ba tsoro a cikin sunan Yesu.
Lao quinene as Barnabé guato gui disipulo sija, ya jasangane sija jaftaemano y liniiña ni y Señot gui chalan ya jacuentuse nu güiya, ya jaftaemano manpredica matatnga si Saulo güiya Damasco ni y naan Jesus.
28 Saboda haka Shawulu ya zauna tare da su yana kai da kawowa a sake a cikin Urushalima, yana magana gabagadi a cikin sunan Ubangiji.
Ya mañisijaja manjuyong yan manjalom guiya Jerusalem.
29 Ya yi magana ya kuma yi muhawwara da Yahudawa masu jin Hellenanci, amma suka yi ƙoƙarin kashe shi.
Ya japredica matatnga ni y naan Señot Jesus: ya jasangan managuaguat yan y Helenista sija; lao maquequepunoja güe nu sija.
30 Sa’ad da’yan’uwa suka sami labarin wannan, sai suka ɗauke shi zuwa Kaisariya suka aika da shi Tarshish.
Ya anae matungo ni y mañelo, macone güe para Sesarea, ya matago para Tarso.
31 Sa’an nan ikkilisiya ko’ina a Yahudiya, Galili da kuma Samariya ta sami salama. Ta yi ƙarfi; ta kuma ƙarfafa ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ta ƙaru sosai tana rayuwa cikin tsoron Ubangiji.
Ya mangaepas todo y iglesia sija guiya Judea, yan Galilea, yan Samaria, ya manmamanagüe, ya manmamomocat gui minaañao as Señot, yan y minagof y Espiritu Santo, lumamegae.
32 Da Bitrus yake zazzaga ƙasar, sai ya je ya ziyarci tsarkakan da suke a Lidda.
Ya susede anae malofan si Pedro gui todo y lugat, na matogüe locue gui mañantos ni y mañasaga Lydda.
33 A can ya tarar da wani mutum mai suna Eniyas, shanyayye wanda yake kwance kan gado shekara takwas.
Ya mañoda güije un taotao na y naanña si Eneas, na esta ocho años gui cama, sa malango paralitico.
34 Sai Bitrus ya ce masa, “Eniyas, Yesu Kiristi ya warkar da kai. Tashi ka naɗe tabarmarka.” Nan da nan Eniyas ya tashi.
Ya ilegña si Pedro nu güiya: Eneas, si Jesucristo unninajomlo: cajulo ya unfamauleg y camamo. Ya enseguidas cajulo.
35 Duk waɗanda suke zama a Lidda da Sharon suka gan shi suka kuma juyo ga Ubangiji.
Ya todo y mañasaga guiya Lyyda yan. Saron, malie güe; ya jabira sija para y Señot.
36 A Yoffa akwai wata almajira mai suna Tabita (a harshen Girik sunanta shi ne Dokas); ita mai aikin alheri ce kullum, tana kuma taimakon matalauta.
Ya guaja un disipulo guiya Joppe, na y naanña Tabita: na comequeilegña Dorcas; este na palaoan bula manmauleg na chocho, yan limosna sija ni y finatinasña.
37 A lokacin nan ta yi rashin lafiya ta mutu, aka kuma yi wa gawarta wanka aka ajiye a wani ɗaki a gidan sama.
Ya ayo sija na jaane, mumalango, ya matae; ya anae munjayan mafagase, mapolo gui aposento gui san jilo.
38 Lidda yana kusa da Yoffa; saboda haka sa’ad da almajirai suka ji cewa Bitrus yana a Lidda, sai suka aiki mutum biyu wurinsa su roƙe shi cewa, “In ka yarda ka zo nan da nan!”
Ya como jijot Lydda guiya Joppe, ya majungog ni y disipulo sija na gaegue güije si Pedro, matago dos taotao para iya güiya, para umagagao: munga atrasao na ufato guiya jame.
39 Sai Bitrus ya tafi tare da su, sa’ad da ya iso sai aka kai shi ɗakin saman. Duka gwauraye suka tsaya kewaye da shi, suna kuka suna nunnuna masa riguna da kuma waɗansu tufafin da Dokas ta yi yayinda take tare da su.
Ayonae cajulo si Pedro, ya jumanao mañisija. Ya anae matogüe, macone guato gui aposento gui san jilo; ya todo y manbiuda manotojgue gui oriyaña ya manatanges ya mafanue ni y magago sija ni y finatinas Dorcas anae manisija.
40 Bitrus ya fitar da su duka daga ɗakin; sa’an nan ya durƙusa ya yi addu’a. Da ya juya wajen matacciyar, sai ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe idanunta, ta ga Bitrus sai ta tashi zaune.
Lao ninafañuja as Pedro, ya dumimo ya manaetae; ya jabira güe guato gui tataotao, ya ilegña: Tabita, cajulo. Ya jababa y atadogña: ya anae jalie si Pedro matachong julo.
41 Ya kama ta a hannu ya taimake ta ta tsaya a ƙafafunta. Sa’an nan ya kira masu bi da kuma gwaurayen ya miƙa musu ita da rai.
Ya janae si Pedro ni y canaeña, ya jinatsa güe julo; ya si Pedro jaagang todo y mañantos yan y manbiuda, ya japresenta na lâlâ.
42 Wannan ya zama sananne ko’ina a Yoffa, mutane da yawa kuma suka gaskata da Ubangiji.
Ya matungo todo guiya Joppe; ya megae manmanjonggue ni y Señot.
43 Bitrus ya zauna a Yoffa na ɗan lokaci tare da wani mai aikin fatu mai suna Siman.
Ya susede na sumaga si Pedro guiya Joppe megae na jaane gui guima un taotao na y naanña si Simon titumo.

< Ayyukan Manzanni 9 >