< Ayyukan Manzanni 8 >

1 Shawulu kuwa yana can, yana tabbatar da mutuwarsa. A wannan rana wani babban tsanani ya auka wa ikkilisiyar da take a Urushalima, sai duka suka warwatsu ko’ina a Yahudiya da Samariya, manzanni kaɗai ne suka rage.
و سولُس با کشته شدن استیفان موافق بود. از آن روز به بعد، شکنجه و آزار ایمانداران کلیسای اورشلیم شروع شد. به طوری که همه به یهودیه و سامره فرار کردند. فقط رسولان در اورشلیم باقی ماندند.
2 Mutane masu tsoron Allah suka binne Istifanus suka kuma yi makoki ƙwarai dominsa.
ولی چند یهودی خداشناس جمع شدند و جنازهٔ استیفان را به خاک سپردند. ایشان از این پیش‌آمد بسیار اندوهگین بودند.
3 Amma Shawulu ya fara hallaka ikkilisiya. Yana shiga gida-gida, yana jan maza da mata yana jefa su cikin kurkuku.
اما سولُس همه جا می‌رفت و ایمانداران به مسیح را شکنجه می‌داد. او خانه به خانه می‌گشت و مردان و زنان را به زور بیرون می‌کشید و به زندان می‌انداخت.
4 Waɗanda aka wartsar suka yi ta wa’azin maganar a duk inda suka tafi.
ولی ایماندارانی که از اورشلیم گریخته بودند، به هر جا می‌رفتند خبر خوش دربارۀ عیسی را به مردم می‌رساندند.
5 Filibus ya gangara zuwa wani birni a Samariya ya kuma yi shelar Kiristi a can.
فیلیپ نیز به یکی از شهرهای سامره رفت و دربارۀ مسیح با اهالی آنجا سخن گفت.
6 Sa’ad da taron mutane suka ji Filibus suka kuma ga abubuwan banmamakin da ya yi, sai duk suka mai da hankali sosai ga abin da ya faɗa.
مردم، به خاطر معجزات او، به دقت به سخنان او گوش می‌دادند.
7 Mugayen ruhohi suka fiffito suna kururuwa daga cikin mutane da yawa, shanyayyu da guragu masu yawa suka sami warkarwa.
ارواح پلید نیز با فریادهای بلند از وجود دیوزدگان بیرون می‌آمدند، و مفلوجان و لنگان شفا می‌یافتند.
8 Saboda haka aka yi farin ciki ƙwarai a birnin.
از این جهت، آن شهر غرق در شادی شد!
9 To, akwai wani mutum mai suna Siman wanda ya kwana biyu yana yin sihiri a birnin har ya ba wa duk mutanen Samariya mamaki. Ya kuma yi taƙama cewa shi wani mai girma ne,
در این میان، در شهر سامره مردی بود به نام شمعون که سالهای سال جادوگری می‌کرد و مردم را به حیرت وا می‌داشت و ادعا می‌کرد که شخص بزرگی است.
10 dukan mutane kuwa, manyan da ƙanana, suka mai da hankali gare shi suka kuma ce, “Mutumin nan shi ne ikon Allah da aka sani a matsayin Iko Mai Girma”
همگان، از کوچک و بزرگ، از او به عنوان «قدرت عظیم خدا» یاد می‌کردند.
11 Suka bi shi domin ya daɗe yana ba su mamaki da sihirinsa.
ایشان به‌دقت به سخنان او گوش فرا می‌دادند، زیرا وی برای مدتی طولانی با چشم‌بندی‌هایش باعث شگفتی آنان شده بود.
12 Amma da suka gaskata da Filibus sa’ad da yake wa’azin labari mai daɗi na mulkin Allah da kuma sunan Yesu Kiristi, sai aka yi musu baftisma, maza da mata.
اما وقتی مردم به پیغام فیلیپ دربارهٔ ملکوت خدا و عیسی مسیح ایمان آوردند، هم مردان و هم زنان تعمید گرفتند.
13 Siman kansa ya gaskata aka kuma yi masa baftisma. Ya kuma bi Filibus ko’ina, yana mamakin manyan alamu da ayyukan banmamakin da ya gani.
سپس شمعون نیز ایمان آورده، تعمید گرفت. او از فیلیپ جدا نمی‌شد و از معجزات او مات و مبهوت می‌ماند.
14 Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
وقتی رسولان در اورشلیم شنیدند که اهالی سامره پیغام خدا را قبول کرده‌اند، پطرس و یوحنا را به آنجا فرستادند.
15 Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
وقتی ایشان به سامره رسیدند، برای نوایمانان دعا کردند تا روح‌القدس را بیابند،
16 domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
زیرا ایشان فقط به نام عیسای خداوند تعمید گرفته بودند و هنوز روح‌القدس بر هیچ‌یک از ایشان نازل نشده بود.
17 Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.
پس پطرس و یوحنا دستهای خود را بر سر این نوایمانان گذاشتند و ایشان نیز روح‌القدس را یافتند.
18 Sa’ad da Siman ya ga cewa ana ba da Ruhu ta wurin ɗibiya hannuwan manzannin, sai ya miƙa musu kuɗi,
وقتی شمعون دید که با قرار گرفتن دستهای رسولان بر سر مردم، روح‌القدس عطا می‌شود، مبلغی پول نزد پطرس و یوحنا آورد تا این قدرت را بخرد.
19 ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iyawa don kowa na ɗibiya wa hannuwana yă karɓi Ruhu Mai Tsarki.”
او گفت: «به من نیز این قدرت را بدهید تا هر وقت دست بر سر کسی می‌گذارم، روح‌القدس را بیابد!»
20 Bitrus ya amsa ya ce, “Bari kuɗinka ya hallaka tare da kai, domin ka yi tsammani za ka iya saya kyautar Allah da kuɗi!
اما پطرس جواب داد: «پولت با تو نابود باد! گمان می‌کنی هدیهٔ خدا را می‌توان با پول خرید!
21 Ba ruwanka da wannan hidimar, domin zuciyarka ba daidai take a gaban Allah ba.
تو از این نعمت بی‌نصیب هستی، چون دلت نزد خدا پاک نیست.
22 Ka tuba daga wannan mugunta ka kuma yi addu’a ga Ubangiji. Wataƙila zai gafarta maka don irin tunanin da yake a zuciyarka.
از این شرارتِ خود توبه کن و دعا کن تا شاید خدا این افکار ناپاکت را ببخشد.
23 Gama na lura kana cike da ɗacin rai kana kuma daure cikin zunubi.”
زیرا می‌بینم که پر از حسادت تلخ و اسیر گناه هستی!»
24 Sai Siman ya amsa ya ce, “Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda ni don kada ko ɗaya daga cikin abin da ka faɗa ya same ni.”
شمعون با التماس گفت: «برای من دعا کنید تا بلایی بر سرم نیاید!»
25 Sa’ad da suka yi shaidar suka kuma yi shelar maganar Ubangiji, sai Bitrus da Yohanna suka koma Urushalima, suna wa’azin bishara a ƙauyukan Samariya masu yawa.
پطرس و یوحنا آنچه را که خدا در زندگی آنان کرده بود، برای ایمانداران سامره تعریف کردند و کلام خداوند را به آنان تعلیم دادند. آنگاه به اورشلیم بازگشتند. سر راهشان به چند روستا نیز سر زدند و پیغام خدا را به اهالی آنجا نیز بشارت دادند.
26 To wani mala’ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Ka yi kudu zuwa hanyar, hanyar hamada, da ta gangara daga Urushalima zuwa Gaza.”
پس از این واقعه، فرشتهٔ خداوند به فیلیپ گفت: «برخیز و رو به جنوب، به راهی برو که از اورشلیم به بیابان غزه می‌رود.»
27 Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
پس فیلیپ به طرف آن جاده به راه افتاد. وقتی به آنجا رسید به خزانه‌دار مملکت حبشه برخورد که در دربار «کنداکه»، ملکهٔ حبشه، نفوذ و قدرت فراوانی داشت. او برای عبادت در معبد به اورشلیم رفته بود،
28 a kan hanyarsa ta komawa gida kuwa yana zaune bisan keken yaƙinsa yana karatun littafin annabin Ishaya.
و اکنون با کالسکه به وطن خود بازمی‌گشت. در ضمن کتاب اشعیای نبی را با صدای بلند می‌خواند.
29 Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa wurin kekunan yaƙin nan ka yi kusa da ita.”
روح خدا به فیلیپ گفت: «تندتر برو تا به کالسکه برسی.»
30 Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, “Ka fahimci abin da kake karantawa?”
فیلیپ جلو دوید و شنید که چه می‌خواند. پس پرسید: «آیا آنچه را که می‌خوانید درک می‌کنید؟»
31 Sai ya ce, “Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?” Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
مرد حبشی جواب داد: «نه، وقتی کسی نیست به من بیاموزد، چگونه می‌توانم درک کنم؟» پس، از فیلیپ خواهش کرد که سوار کالسکه شود و کنار او بنشیند.
32 Bābān yana karanta wannan Nassin, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka, kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru, haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.
آن قسمتی که از کتب مقدّس می‌خواند، این بود: «همچنانکه گوسفند را به سوی کشتارگاه می‌برند، او را نیز به کشتارگاه بردند. او مثل بره‌ای که پشمهایش را می‌چینند، لب به اعتراض نگشود.
33 A cikin wulaƙacinsa aka hana masa gaskiya. Wa zai iya yin zancen zuriyarsa? Gama an ɗauke ransa daga duniya.”
او فروتن بود؛ از این رو هرگونه بی‌عدالتی در حق او روا داشتند. چه کسی می‌تواند از نسل او سخن بگوید؟ زیرا حیات او از زمین برداشته شد.»
34 Sai bābān ya tambayi Filibus ya ce, “Ka gaya mini, ina roƙonka, annabin yana magana a kan wane ne, kansa ne, ko kuwa wani dabam?”
خزانه‌دار حبشی از فیلیپ پرسید: «آیا اشعیا این چیزها را دربارهٔ خودش می‌گفت یا دربارهٔ شخص دیگری؟»
35 Sa’an nan Filibus ya fara da wannan Nassi ɗin ya kuma faɗa masa labari mai daɗi game da Yesu.
آنگاه فیلیپ از آن نوشتهٔ مقدّس شروع کرد و با استفاده از قسمتهای دیگر کتاب‌مقدّس، پیام نجاتبخش عیسی را به او رسانید.
36 Yayinda suke cikin tafiya a kan hanya, sai suka iso wani wurin ruwa bābān nan ya ce, “Duba, ga ruwa. Me zai hana a yi mini baftisma?”
همچنانکه کالسکه پیش می‌رفت، به یک برکهٔ آب رسیدند. مرد حبشی گفت: «نگاه کن! این هم آب! آیا امکان دارد حالا تعمید بگیرم؟»
فیلیپ جواب داد: «اگر با تمام وجودت ایمان آورده‌ای، امکان دارد.» جواب داد: «من ایمان دارم که عیسی مسیح، پسر خداست.»
38 Ya kuwa ba da umarni a tsai da keken yaƙin. Sa’an nan da Filibus da bābān suka gangara zuwa cikin ruwan Filibus kuwa ya yi masa baftisma.
پس کالسکه را نگاه داشتند و هر دو داخل آب رفتند و فیلیپ او را تعمید داد.
39 Sa’ad da suka fita daga cikin ruwan, sai Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuwa bai ƙara ganinsa ba, amma ya ci gaba da tafiyarsa yana farin ciki.
وقتی از آب بیرون آمدند، روح خداوند فیلیپ را برداشت و برد و خزانه‌دار حبشی دیگر او را ندید، ولی راه خود را با خوشحالی پیش گرفت و رفت.
40 Filibus kuwa ya fito a Azotus, ya yi ta zagawa, yana wa’azin bishara a dukan garuruwan sai da ya kai Kaisariya.
اما فیلیپ در شهر اشدود دیده شد. پس هم در آنجا و هم در شهرهای سر راه خود، پیغام خدا را به مردم رساند تا به شهر قیصریه رسید.

< Ayyukan Manzanni 8 >