< Ayyukan Manzanni 8 >

1 Shawulu kuwa yana can, yana tabbatar da mutuwarsa. A wannan rana wani babban tsanani ya auka wa ikkilisiyar da take a Urushalima, sai duka suka warwatsu ko’ina a Yahudiya da Samariya, manzanni kaɗai ne suka rage.
Saulus oli seal ja kiitis tema surma heaks. Sel päeval algas Jeruusalemmas suur koguduse tagakiusamine ja kõik peale apostlite pillutati laiali Juudamaal ja Samaarias.
2 Mutane masu tsoron Allah suka binne Istifanus suka kuma yi makoki ƙwarai dominsa.
Jumalakartlikud mehed matsid Stefanose ja nutsid valjult tema pärast.
3 Amma Shawulu ya fara hallaka ikkilisiya. Yana shiga gida-gida, yana jan maza da mata yana jefa su cikin kurkuku.
Ent Saulus hakkas hävitama kogudust. Majast majja liikudes tiris ta välja nii mehi kui naisi ja pani nad vangi.
4 Waɗanda aka wartsar suka yi ta wa’azin maganar a duk inda suka tafi.
Need, kes olid laiali pillutatud, kuulutasid sõna igal pool, kuhu nad läksid.
5 Filibus ya gangara zuwa wani birni a Samariya ya kuma yi shelar Kiristi a can.
Filippus läks alla ühte Samaaria linna ja kuulutas seal Messiat.
6 Sa’ad da taron mutane suka ji Filibus suka kuma ga abubuwan banmamakin da ya yi, sai duk suka mai da hankali sosai ga abin da ya faɗa.
Rahvas kuulas Filippust, nad panid tähele tema sõnu ja nägid tunnustähti, mida ta tegi.
7 Mugayen ruhohi suka fiffito suna kururuwa daga cikin mutane da yawa, shanyayyu da guragu masu yawa suka sami warkarwa.
Sest paljudest lahkusid kurjad vaimud kisendades, palju halvatuid ja jalutuid aga sai terveks.
8 Saboda haka aka yi farin ciki ƙwarai a birnin.
Suur rõõm oli kogu linnas.
9 To, akwai wani mutum mai suna Siman wanda ya kwana biyu yana yin sihiri a birnin har ya ba wa duk mutanen Samariya mamaki. Ya kuma yi taƙama cewa shi wani mai girma ne,
Juba mõnda aega oli seal linnas elanud mees nimega Siimon, kes tegeles nõidumisega ja pani Samaaria inimesi jahmuma. Ta pidas ennast tähtsaks.
10 dukan mutane kuwa, manyan da ƙanana, suka mai da hankali gare shi suka kuma ce, “Mutumin nan shi ne ikon Allah da aka sani a matsayin Iko Mai Girma”
Talle pöörasid tähelepanu kõik inimesed, nii kõrged kui madalad, ning kuulutasid: „Seda meest nimetatakse Jumala Suureks Väeks!“
11 Suka bi shi domin ya daɗe yana ba su mamaki da sihirinsa.
Nad järgisid teda, sest ta oli neid oma nõiakunstiga kaua aega hämmastanud.
12 Amma da suka gaskata da Filibus sa’ad da yake wa’azin labari mai daɗi na mulkin Allah da kuma sunan Yesu Kiristi, sai aka yi musu baftisma, maza da mata.
Aga kui nad hakkasid uskuma Filippust, kes neile kuulutas evangeeliumi Jumala riigist ja Jeesuse Kristuse nimest, siis ristiti nii mehi kui naisi.
13 Siman kansa ya gaskata aka kuma yi masa baftisma. Ya kuma bi Filibus ko’ina, yana mamakin manyan alamu da ayyukan banmamakin da ya gani.
Ka Siimon uskus ja sai ristitud. Ta hoidis Filippuse ligi kõikjal, olles hämmastunud tema läbi sündinud vägevatest tunnustähtedest ja imedest.
14 Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
Kui apostlid kuulsid Jeruusalemmas, et Samaaria oli Jumala sõna vastu võtnud, läkitasid nad nende juurde Peetruse ja Johannese.
15 Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
Sinna jõudes palvetasid nad samaarlaste eest, et nad saaksid Püha Vaimu.
16 domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
Sest Vaim ei olnud veel langenud kellegi peale neist, nad oli üksnes ristitud Issanda Jeesuse nimesse.
17 Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.
Siis panid Peetrus ja Johannes oma käed nende peale ja nad said Püha Vaimu.
18 Sa’ad da Siman ya ga cewa ana ba da Ruhu ta wurin ɗibiya hannuwan manzannin, sai ya miƙa musu kuɗi,
Aga kui Siimon nägi, et Vaim antakse apostlite käte pealepanemise kaudu, pakkus ta neile raha
19 ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iyawa don kowa na ɗibiya wa hannuwana yă karɓi Ruhu Mai Tsarki.”
ja ütles: „Andke mulle ka see meelevald, et igaüks saaks Püha Vaimu, kelle peale ma oma käed panen!“
20 Bitrus ya amsa ya ce, “Bari kuɗinka ya hallaka tare da kai, domin ka yi tsammani za ka iya saya kyautar Allah da kuɗi!
Peetrus vastas: „Hävigu su hõbe koos sinuga, et sa mõtled Jumala andi saada raha eest!
21 Ba ruwanka da wannan hidimar, domin zuciyarka ba daidai take a gaban Allah ba.
Sul ei ole mingit osa sellest sõnast, sest su süda ei ole õige Jumala ees.
22 Ka tuba daga wannan mugunta ka kuma yi addu’a ga Ubangiji. Wataƙila zai gafarta maka don irin tunanin da yake a zuciyarka.
Seepärast paranda meelt oma kurjusest ja anu Issandat. Ehk ta andestab sulle, et oled säärast mõtet oma südames mõelnud.
23 Gama na lura kana cike da ɗacin rai kana kuma daure cikin zunubi.”
Sest ma näen sind kibeduses ja ebaõigluse kammitsais.“
24 Sai Siman ya amsa ya ce, “Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda ni don kada ko ɗaya daga cikin abin da ka faɗa ya same ni.”
Siimon aga vastas: „Paluge teie Issandat minu pärast, et minu peale ei langeks midagi sellest, mis te olete öelnud!“
25 Sa’ad da suka yi shaidar suka kuma yi shelar maganar Ubangiji, sai Bitrus da Yohanna suka koma Urushalima, suna wa’azin bishara a ƙauyukan Samariya masu yawa.
Kui apostlid olid tunnistanud ja rääkinud Issanda sõna, pöördusid nad tagasi Jeruusalemma ja kuulutasid evangeeliumi paljudes Samaaria külades.
26 To wani mala’ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Ka yi kudu zuwa hanyar, hanyar hamada, da ta gangara daga Urushalima zuwa Gaza.”
Issanda ingel ütles Filippusele: „Tõuse ja mine lõuna poole seda teed, mis läheb Jeruusalemmast alla Gazasse, see on kõrbetee!“
27 Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
Nõnda ta asus teele. Ja vaata, oma teel kohtas ta Etioopia eunuhhi, kes valitses etiooplaste kuninganna Kandake kogu varanduse üle. See mees oli tulnud Jeruusalemma Jumalat kummardama
28 a kan hanyarsa ta komawa gida kuwa yana zaune bisan keken yaƙinsa yana karatun littafin annabin Ishaya.
ning oli tagasi pöördumas koju ja istus oma kaarikus ja luges prohvet Jesaja raamatut.
29 Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa wurin kekunan yaƙin nan ka yi kusa da ita.”
Jumala Vaim ütles Filippusele: „Mine kaariku juurde ja püsi selle lähedal!“
30 Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, “Ka fahimci abin da kake karantawa?”
Filippus jooksis kaariku juurde ja kuulis meest lugemas prohvet Jesaja raamatut. „Kas sa ka mõistad, mida sa loed?“küsis Filippus.
31 Sai ya ce, “Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?” Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
„Kuidas ma saan mõista, “ta ütles, „ilma et keegi mulle selgitaks?“Ja ta kutsus Filippuse üles enda kõrvale istuma.
32 Bābān yana karanta wannan Nassin, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka, kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru, haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.
Eunuhh oli parasjagu lugemas seda kirjakohta: „Nagu lammas viidi ta tappa, ja nagu tall oma niitja ees on vait, nõnda ei avanud ta oma suud!
33 A cikin wulaƙacinsa aka hana masa gaskiya. Wa zai iya yin zancen zuriyarsa? Gama an ɗauke ransa daga duniya.”
Tema alandamisega on tema õigus ära võetud. Kes jõuab tema suguvõsast jutustada? Sest ta elu võetakse ära maa pealt.“
34 Sai bābān ya tambayi Filibus ya ce, “Ka gaya mini, ina roƙonka, annabin yana magana a kan wane ne, kansa ne, ko kuwa wani dabam?”
Eunuhh küsis Filippuselt: „Palun ütle mulle, kellest prohvet siin räägib, kas endast või kellestki teisest?“
35 Sa’an nan Filibus ya fara da wannan Nassi ɗin ya kuma faɗa masa labari mai daɗi game da Yesu.
Ja Filippus alustas samast kirjakohast ja kuulutas talle evangeeliumi Jeesusest.
36 Yayinda suke cikin tafiya a kan hanya, sai suka iso wani wurin ruwa bābān nan ya ce, “Duba, ga ruwa. Me zai hana a yi mini baftisma?”
Kui nad teed mööda edasi sõitsid, jõudsid nad veekoguni ja eunuhh ütles: „Vaata, vesi! Mis takistab mind saama ristitud?“
Filippus vastas: „Kui sa usud kogu südamest, siis on see võimalik!“Mees vastas: „Mina usun, et Jeesus Kristus on Jumala Poeg!“
38 Ya kuwa ba da umarni a tsai da keken yaƙin. Sa’an nan da Filibus da bābān suka gangara zuwa cikin ruwan Filibus kuwa ya yi masa baftisma.
Ja ta käskis kaariku peatada. Nii Filippus kui eunuhh astusid vette ja Filippus ristis tema.
39 Sa’ad da suka fita daga cikin ruwan, sai Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuwa bai ƙara ganinsa ba, amma ya ci gaba da tafiyarsa yana farin ciki.
Aga kui nad veest välja tulid, võttis Issanda Vaim Filippuse ära, ja eunuhh ei näinud teda enam; kuid ta läks oma teed edasi rõõmuga.
40 Filibus kuwa ya fito a Azotus, ya yi ta zagawa, yana wa’azin bishara a dukan garuruwan sai da ya kai Kaisariya.
Aga Filippus leiti Asdodist, ja ta kuulutas evangeeliumi kõigile linnadele, kuni ta jõudis Kaisareasse.

< Ayyukan Manzanni 8 >