< Ayyukan Manzanni 8 >

1 Shawulu kuwa yana can, yana tabbatar da mutuwarsa. A wannan rana wani babban tsanani ya auka wa ikkilisiyar da take a Urushalima, sai duka suka warwatsu ko’ina a Yahudiya da Samariya, manzanni kaɗai ne suka rage.
Men Saulus fandt Behag i hans Mord. Og paa den Dag udbrød der en stor Forfølgelse imod Menigheden i Jerusalem, og de adspredtes alle over Judæas og Samarias Egne, undtagen Apostlene.
2 Mutane masu tsoron Allah suka binne Istifanus suka kuma yi makoki ƙwarai dominsa.
Men gudfrygtige Mænd begravede Stefanus og holdt en stor Veklage over ham.
3 Amma Shawulu ya fara hallaka ikkilisiya. Yana shiga gida-gida, yana jan maza da mata yana jefa su cikin kurkuku.
Men Saulus plagede Menigheden og gik ind i Husene og trak baade Mænd og Kvinder frem og lod dem sætte i Fængsel.
4 Waɗanda aka wartsar suka yi ta wa’azin maganar a duk inda suka tafi.
Imidlertid gik de, som bleve adspredte, omkring og forkyndte Evangeliets Ord.
5 Filibus ya gangara zuwa wani birni a Samariya ya kuma yi shelar Kiristi a can.
Da kom Filip til Byen Samaria og prædikede Kristus for dem.
6 Sa’ad da taron mutane suka ji Filibus suka kuma ga abubuwan banmamakin da ya yi, sai duk suka mai da hankali sosai ga abin da ya faɗa.
Og Skarerne gave endrægtigt Agt paa det, som blev sagt af Filip, idet de hørte og saa de Tegn, som han gjorde.
7 Mugayen ruhohi suka fiffito suna kururuwa daga cikin mutane da yawa, shanyayyu da guragu masu yawa suka sami warkarwa.
Thi der var mange, som havde urene Aander, og af hvem disse fore ud, raabende med høj Røst; og mange værkbrudne og lamme bleve helbredede.
8 Saboda haka aka yi farin ciki ƙwarai a birnin.
Og der blev en stor Glæde i denne By.
9 To, akwai wani mutum mai suna Siman wanda ya kwana biyu yana yin sihiri a birnin har ya ba wa duk mutanen Samariya mamaki. Ya kuma yi taƙama cewa shi wani mai girma ne,
Men en Mand, ved Navn Simon, var i Forvejen i Byen og drev Trolddom og satte Samarias Folk i Forbavselse, idet han udgav sig selv for at være noget stort.
10 dukan mutane kuwa, manyan da ƙanana, suka mai da hankali gare shi suka kuma ce, “Mutumin nan shi ne ikon Allah da aka sani a matsayin Iko Mai Girma”
Paa ham gave alle Agt, smaa og store, og sagde: „Det er ham, som man kalder Guds store Kraft.”
11 Suka bi shi domin ya daɗe yana ba su mamaki da sihirinsa.
Men de gave Agt paa ham, fordi han i lang Tid havde sat dem i Forbavselse ved sine Trolddomskunster.
12 Amma da suka gaskata da Filibus sa’ad da yake wa’azin labari mai daɗi na mulkin Allah da kuma sunan Yesu Kiristi, sai aka yi musu baftisma, maza da mata.
Men da de troede Filip, som forkyndte Evangeliet om Guds Rige og Jesu Kristi Navn, lode de sig døbe, baade Mænd og Kvinder.
13 Siman kansa ya gaskata aka kuma yi masa baftisma. Ya kuma bi Filibus ko’ina, yana mamakin manyan alamu da ayyukan banmamakin da ya gani.
Men Simon troede ogsaa selv, og efter at være døbt holdt han sig nær til Filip; og da han saa Tegn og store kraftige Gerninger ske, forbavsedes han højligt.
14 Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
Men da Apostlene i Jerusalem hørte, at Samaria havde taget imod Guds Ord, sendte de Peter og Johannes til dem,
15 Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
og da disse vare komne derned, bade de for dem om, at de maatte faa den Helligaand;
16 domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
thi den var endnu ikke falden paa nogen af dem, men de vare blot døbte til den Herres Jesu Navn.
17 Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.
Da lagde de Hænderne paa dem, og de fik den Helligaand.
18 Sa’ad da Siman ya ga cewa ana ba da Ruhu ta wurin ɗibiya hannuwan manzannin, sai ya miƙa musu kuɗi,
Men da Simon saa, at den Helligaand blev given ved Apostlenes Haandspaalæggelse, bragte han dem Penge og sagde:
19 ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iyawa don kowa na ɗibiya wa hannuwana yă karɓi Ruhu Mai Tsarki.”
„Giver ogsaa mig denne Magt, at, hvem jeg lægger Hænderne paa, han maa faa den Helligaand.”
20 Bitrus ya amsa ya ce, “Bari kuɗinka ya hallaka tare da kai, domin ka yi tsammani za ka iya saya kyautar Allah da kuɗi!
Men Peter sagde til ham: „Gid dit Sølv maa gaa til Grunde tillige med dig, fordi du mente at kunne erhverve Guds Gave for Penge.
21 Ba ruwanka da wannan hidimar, domin zuciyarka ba daidai take a gaban Allah ba.
Du har ikke Del eller Lod i dette Ord; thi dit Hjerte er ikke ret for Gud.
22 Ka tuba daga wannan mugunta ka kuma yi addu’a ga Ubangiji. Wataƙila zai gafarta maka don irin tunanin da yake a zuciyarka.
Omvend dig derfor fra denne din Ondskab og bed Herren, om dog dit Hjertes Paafund maatte forlades dig.
23 Gama na lura kana cike da ɗacin rai kana kuma daure cikin zunubi.”
Thi jeg ser, at du er stedt i Bitterheds Galde og Uretfærdigheds Lænke.”
24 Sai Siman ya amsa ya ce, “Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda ni don kada ko ɗaya daga cikin abin da ka faɗa ya same ni.”
Men Simon svarede og sagde: „Beder I for mig til Herren, for at intet af det, som I have sagt, skal komme over mig.”
25 Sa’ad da suka yi shaidar suka kuma yi shelar maganar Ubangiji, sai Bitrus da Yohanna suka koma Urushalima, suna wa’azin bishara a ƙauyukan Samariya masu yawa.
Men da de havde vidnet og talt Herrens Ord, vendte de tilbage til Jerusalem, og de forkyndte Evangeliet i mange af Samaritanernes Landsbyer.
26 To wani mala’ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Ka yi kudu zuwa hanyar, hanyar hamada, da ta gangara daga Urushalima zuwa Gaza.”
Men en Herrens Engel talte til Filip og sagde: „Staa op og gaa mod Syd paa den Vej, som gaar ned fra Jerusalem til Gaza; den er øde.”
27 Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
Og han stod op og gik. Og se, der var en Æthioper, en Hofmand, en mægtig Mand hos Kandake, Æthiopernes Dronning, som var sat over alle hendes Skatte; han var kommen til Jerusalem for at tilbede.
28 a kan hanyarsa ta komawa gida kuwa yana zaune bisan keken yaƙinsa yana karatun littafin annabin Ishaya.
Og han var paa Hjemvejen og sad paa sin Vogn og læste Profeten Esajas.
29 Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa wurin kekunan yaƙin nan ka yi kusa da ita.”
Men Aanden sagde til Filip: „Gaa hen og hold dig til denne Vogn!”
30 Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, “Ka fahimci abin da kake karantawa?”
Og Filip løb derhen og hørte ham læse Profeten Esajas; og han sagde: „Forstaar du ogsaa det, som du læser?”
31 Sai ya ce, “Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?” Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
Men han sagde: „Hvorledes skulde jeg kunne det, uden nogen vejleder mig?” Og han bad Filip stige op og sætte sig hos ham.
32 Bābān yana karanta wannan Nassin, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka, kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru, haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.
Men det Stykke af Skriften, som han læste, var dette: „Som et Faar blev han ført til Slagtning, og som et Lam er stumt imod den, der klipper det, saaledes oplader han ej sin Mund.
33 A cikin wulaƙacinsa aka hana masa gaskiya. Wa zai iya yin zancen zuriyarsa? Gama an ɗauke ransa daga duniya.”
I Fornedrelsen blev hans Dom taget bort; hvem kan fortælle om hans Slægt, efterdi hans Liv borttages fra Jorden?”
34 Sai bābān ya tambayi Filibus ya ce, “Ka gaya mini, ina roƙonka, annabin yana magana a kan wane ne, kansa ne, ko kuwa wani dabam?”
Men Hofmanden talte til Filip og sagde: „Jeg beder dig, om hvem siger Profeten dette? om sig selv eller om en anden?”
35 Sa’an nan Filibus ya fara da wannan Nassi ɗin ya kuma faɗa masa labari mai daɗi game da Yesu.
Da oplod Filip sin Mund, og idet han begyndte fra dette Skriftsted, forkyndte han ham Evangeliet om Jesus.
36 Yayinda suke cikin tafiya a kan hanya, sai suka iso wani wurin ruwa bābān nan ya ce, “Duba, ga ruwa. Me zai hana a yi mini baftisma?”
Men som de droge frem ad Vejen, kom de til noget Vand; og Hofmanden siger: „Se, her er Vand, hvad hindrer mig fra at blive døbt?”
[Men Filip sagde: „Dersom du tror af hele dit Hjerte, kan det ske.” Men han svarede og sagde: „Jeg tror, at Jesus Kristus er Guds Søn.”]
38 Ya kuwa ba da umarni a tsai da keken yaƙin. Sa’an nan da Filibus da bābān suka gangara zuwa cikin ruwan Filibus kuwa ya yi masa baftisma.
Og han bød, at Vognen skulde holde, og de stege begge ned i Vandet, baade Filip og Hofmanden; og han døbte ham.
39 Sa’ad da suka fita daga cikin ruwan, sai Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuwa bai ƙara ganinsa ba, amma ya ci gaba da tafiyarsa yana farin ciki.
Men da de stege op af Vandet, bortrykkede Herrens Aand Filip, og Hofmanden saa ham ikke mere; thi han drog sin Vej med Glæde.
40 Filibus kuwa ya fito a Azotus, ya yi ta zagawa, yana wa’azin bishara a dukan garuruwan sai da ya kai Kaisariya.
Men Filip blev funden i Asdod, og han drog omkring og forkyndte Evangeliet i alle Byerne, indtil han kom til Kæsarea.

< Ayyukan Manzanni 8 >