< Ayyukan Manzanni 8 >
1 Shawulu kuwa yana can, yana tabbatar da mutuwarsa. A wannan rana wani babban tsanani ya auka wa ikkilisiyar da take a Urushalima, sai duka suka warwatsu ko’ina a Yahudiya da Samariya, manzanni kaɗai ne suka rage.
扫罗也认可了对司提芬的杀戮。从那天起,耶路撒冷的教会受到严重迫害。除了使徒以外,其他信徒都散落到犹太和撒玛利亚各地。
2 Mutane masu tsoron Allah suka binne Istifanus suka kuma yi makoki ƙwarai dominsa.
(有些虔诚之人怀着巨大的悲痛安葬了司提芬)。
3 Amma Shawulu ya fara hallaka ikkilisiya. Yana shiga gida-gida, yana jan maza da mata yana jefa su cikin kurkuku.
扫罗却开始残害教会,挨家挨户地将男男女女拖出去坐监。
4 Waɗanda aka wartsar suka yi ta wa’azin maganar a duk inda suka tafi.
那些散落各地的信徒,会在所到之处传扬上帝之道。
5 Filibus ya gangara zuwa wani birni a Samariya ya kuma yi shelar Kiristi a can.
腓利来到了撒玛利亚城,向民众宣讲基督。
6 Sa’ad da taron mutane suka ji Filibus suka kuma ga abubuwan banmamakin da ya yi, sai duk suka mai da hankali sosai ga abin da ya faɗa.
群众听到腓利所讲,看见他所行神迹,于是便全心聆听他的一字一句。
7 Mugayen ruhohi suka fiffito suna kururuwa daga cikin mutane da yawa, shanyayyu da guragu masu yawa suka sami warkarwa.
许多魔鬼附体之人得救了,他们身上的恶灵嚎叫着被驱赶出来,还有许多瘫痪和残疾之人都得到痊愈。
8 Saboda haka aka yi farin ciki ƙwarai a birnin.
城里的民众们欢天喜地。
9 To, akwai wani mutum mai suna Siman wanda ya kwana biyu yana yin sihiri a birnin har ya ba wa duk mutanen Samariya mamaki. Ya kuma yi taƙama cewa shi wani mai girma ne,
城里有一人名叫西门,善用邪术。他自称是一位重要的大人物,让撒玛利亚人为之而惊叹。
10 dukan mutane kuwa, manyan da ƙanana, suka mai da hankali gare shi suka kuma ce, “Mutumin nan shi ne ikon Allah da aka sani a matsayin Iko Mai Girma”
城中之人无论高高在上还是卑微在下,都听从于他,说:“这就是那‘大能上帝’之人。”
11 Suka bi shi domin ya daɗe yana ba su mamaki da sihirinsa.
因为他长久以来用邪术蒙蔽众人,让他们对之感到信服。
12 Amma da suka gaskata da Filibus sa’ad da yake wa’azin labari mai daɗi na mulkin Allah da kuma sunan Yesu Kiristi, sai aka yi musu baftisma, maza da mata.
腓利来此向他们传递上帝之国的福音,宣讲耶稣基督之名,于是众人相信了腓利,男女女女均受了洗。
13 Siman kansa ya gaskata aka kuma yi masa baftisma. Ya kuma bi Filibus ko’ina, yana mamakin manyan alamu da ayyukan banmamakin da ya gani.
连西门自己也相信并受洗,然后跟随腓利,为所目睹的神迹和奇迹而惊叹不已。
14 Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
听说撒玛利亚的居民接受了上帝之道,耶路撒冷的使徒就派彼得和约翰到那里去。
15 Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
二人赶到后就为改变信仰的信徒祷告,让他们接受圣灵。
16 domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
但圣灵尚未降在他们任何一个身上,他们只是以耶稣之名受了洗。
17 Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.
使徒为他们行按手礼,他们便接受了圣灵。
18 Sa’ad da Siman ya ga cewa ana ba da Ruhu ta wurin ɗibiya hannuwan manzannin, sai ya miƙa musu kuɗi,
西门看见使徒按手后就有圣灵降临,就拿出钱给使徒,
19 ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iyawa don kowa na ɗibiya wa hannuwana yă karɓi Ruhu Mai Tsarki.”
他请求道:“把这力量也给我吧,让我为谁按手,谁就可以接受圣灵。”
20 Bitrus ya amsa ya ce, “Bari kuɗinka ya hallaka tare da kai, domin ka yi tsammani za ka iya saya kyautar Allah da kuɗi!
彼得对他说:“让你的钱跟你一同灭亡吧!你居然以为上帝的恩赐可以用钱购买!
21 Ba ruwanka da wannan hidimar, domin zuciyarka ba daidai take a gaban Allah ba.
你不属于这里,这里的一切也不属于你,因为在上帝眼中,你的态度大错特错。
22 Ka tuba daga wannan mugunta ka kuma yi addu’a ga Ubangiji. Wataƙila zai gafarta maka don irin tunanin da yake a zuciyarka.
为自己的罪恶行径忏悔吧!祈求主,请求他原谅你这样的想法。
23 Gama na lura kana cike da ɗacin rai kana kuma daure cikin zunubi.”
我可以看出你心中满是强烈的嫉妒,被你的恶所捆绑。”
24 Sai Siman ya amsa ya ce, “Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda ni don kada ko ɗaya daga cikin abin da ka faɗa ya same ni.”
西门回答:“请为我求主,别让你们说的事情发生在我身上!”
25 Sa’ad da suka yi shaidar suka kuma yi shelar maganar Ubangiji, sai Bitrus da Yohanna suka koma Urushalima, suna wa’azin bishara a ƙauyukan Samariya masu yawa.
使徒作了见证并宣讲了主的道,然后就返回耶路撒冷,沿途在撒玛利亚人的许多村庄里传扬福音。
26 To wani mala’ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Ka yi kudu zuwa hanyar, hanyar hamada, da ta gangara daga Urushalima zuwa Gaza.”
主的天使对腓利说:“准备好向南走,你要去耶路撒冷到迦萨的那条荒漠道路。”
27 Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
于是腓利动身出发,路上遇到一名衣索匹亚人,是衣索匹亚女王干大基手下一名位高权重的官员,掌管女王全部国库。他去耶路撒冷去礼拜。
28 a kan hanyarsa ta komawa gida kuwa yana zaune bisan keken yaƙinsa yana karatun littafin annabin Ishaya.
在回来的路上,坐在马车上翻看以赛亚先知的书。
29 Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa wurin kekunan yaƙin nan ka yi kusa da ita.”
圣灵对腓利说:“走过去,走近那车子。”
30 Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, “Ka fahimci abin da kake karantawa?”
于是腓利跑过去,听见那官员在读以赛亚先知的书,就询问:“你明白自己看到的内容吗?”
31 Sai ya ce, “Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?” Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
那官员说:“没有人指导,我怎能明白呢?”于是就请腓利上车,坐在他身边。
32 Bābān yana karanta wannan Nassin, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka, kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru, haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.
他当时在读的那段经文是:“他像绵羊一样被牵走宰杀,又像羔羊一样在剪羊毛之人面前沉默无声,他一句话也不说。
33 A cikin wulaƙacinsa aka hana masa gaskiya. Wa zai iya yin zancen zuriyarsa? Gama an ɗauke ransa daga duniya.”
他受尽屈辱,得不到公平的审判。没有人知道他的后裔会是谁,因为他的生命走向终点。”
34 Sai bābān ya tambayi Filibus ya ce, “Ka gaya mini, ina roƙonka, annabin yana magana a kan wane ne, kansa ne, ko kuwa wani dabam?”
那官员对腓利说:“请问先知这番话是在说谁?他自己?还是指别人?”
35 Sa’an nan Filibus ya fara da wannan Nassi ɗin ya kuma faɗa masa labari mai daɗi game da Yesu.
腓利开始解释,从这段经文开始,向他传讲耶稣。
36 Yayinda suke cikin tafiya a kan hanya, sai suka iso wani wurin ruwa bābān nan ya ce, “Duba, ga ruwa. Me zai hana a yi mini baftisma?”
他们一路走下去,来到一处溪流,官员说:“你看,这里有水,为什么我不受洗呢?”
38 Ya kuwa ba da umarni a tsai da keken yaƙin. Sa’an nan da Filibus da bābān suka gangara zuwa cikin ruwan Filibus kuwa ya yi masa baftisma.
于是官员吩咐停车,腓利和他两人走到水中,腓利给他施洗。
39 Sa’ad da suka fita daga cikin ruwan, sai Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuwa bai ƙara ganinsa ba, amma ya ci gaba da tafiyarsa yana farin ciki.
他们从水里出来时,主的圣灵就把腓利带走了,送到了亚锁都。官员再也没有见到他,但仍满心喜悦地继续旅程。
40 Filibus kuwa ya fito a Azotus, ya yi ta zagawa, yana wa’azin bishara a dukan garuruwan sai da ya kai Kaisariya.
腓利在亚锁都走遍各城,传讲福音,最终来到该撒利亚。