< Ayyukan Manzanni 7 >

1 Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
Tedy rzekł najwyższy kapłan: A także się ma ta rzecz?
2 Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
A on rzekł: Mężowie bracia i ojcowie, słuchajcie! Bóg chwały ukazał się ojcu naszemu Abrahamowi, gdy był w Mezopotamii, przedtem niż mieszkał w Haranie.
3 Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
I rzekł do niego: Wynijdź z ziemi twojej i od twojej rodziny, a idź do ziemi, którą ci ukażę.
4 “Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
Tedy wyszedłszy z ziemi Chaldejskiej, mieszkał w Haranie, a stamtąd, gdy umarł ojciec jego, przeniósł go Bóg do ziemi tej, w której wy teraz mieszkacie.
5 Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
I nie dał mu w niej dziedzictwa i na stopę nogi, choć mu ją był obiecał dać w dzierżawę, i nasieniu jego po nim, gdy jeszcze nie miał potomka.
6 Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
I mówił mu tak Bóg: Nasienie twoje będzie przychodniem w cudzej ziemi i zniewolą je, i trapić je będą przez czterysta lat.
7 Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
Ale ten naród, któremu służyć będą, ja będę sądził, rzekł Bóg; a potem wynijdą i służyć mi będą na tem miejscu.
8 Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
I dał mu przymierze obrzezki; i tak Abraham spłodził Izaaka i obrzezał go dnia ósmego, a Izaak Jakóba, a Jakób dwunastu patryjarchów.
9 “Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
A patryjarchowie nienawidząc Józefa, sprzedali go do Egiptu; ale Bóg był z nim.
10 ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
I wyrwał go ze wszystkich jego ucisków, a dał mu łaskę i mądrość przed Faraonem, królem Egipskim, który go postanowił książęciem nad Egiptem i nad wszystkim domem swoim.
11 “Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
Potem przyszedł głód na wszystkę ziemię Egipską i Chananejską, i ucisk wielki, i nie znajdowali żywności ojcowie nasi.
12 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
A gdy usłyszał Jakób, iż zboża były w Egipcie, posłał ojców naszych pierwszy raz.
13 A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
A za wtórym razem poznany jest Józef od braci swych i objawiony jest Faraonowi naród Józefowy.
14 Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
Tedy Józef posławszy, przyzwał ojca swego Jakóba i wszystkę swoję rodzinę w siedmdziesiąt i pięciu duszach.
15 Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
I zstąpił Jakób do Egiptu, i tam umarł on i ojcowie nasi.
16 Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
I przeniesieni są do Sychem, i położeni w grobie, który był kupił Abraham za pieniądze u synów Hemora, ojca Sychemowego.
17 “Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
A gdy się przybliżył czas obietnicy, o którą był przysiągł Bóg Abrahamowi, rozrodził się lud i rozmnożył się w Egipcie.
18 Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
Aż nastał inny król, który nie znał Józefa.
19 Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
Ten podchodząc zdradliwie naród nasz, trapił ojców naszych, tak iż musieli wymiatać niemowlątka swoje, żeby się nie rozkrzewiały.
20 “A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
Pod ten czas narodził się Mojżesz, a był krasnym z daru Bożego, którego chowano przez trzy miesiące w domu ojca jego.
21 Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
A gdy był wyrzucony, wzięła go córka Faraonowa i wychowała go sobie za syna.
22 Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
I wyćwiczony jest Mojżesz we wszelkiej mądrości Egipskiej, a był możny w mowach i w uczynkach.
23 “Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
A gdy mu było czterdzieści lat, przyszło mu na myśl, aby nawiedził braci swych, syny Izraelskie.
24 Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
A ujrzawszy jednego ukrzywdzonego, ujął się oń i pomścił się krzywdy tego, który bezprawie cierpiał, zabiwszy Egipczanina.
25 Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
Albowiem mniemał, że bracia jego rozumieją, że Bóg przez rękę jego daje im wybawienie; lecz oni tego nie rozumieli.
26 Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
A nazajutrz pokazał się im, gdy się z sobą bili i prowadził je do pokoju, mówiąc: Mężowie! bracia jesteście sobie; przeczże się społem krzywdzicie?
27 “Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
Lecz ten, co krzywdził bliźniego, odegnał go, mówiąc: Któż cię postanowił książęciem i sędzią nad nami?
28 Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
Izali mię ty chcesz zabić, jakoś wczoraj zabił Egipczanina?
29 Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
I uciekł Mojżesz za temi słowy i był przychodniem w ziemi Madyjańskiej, gdzie spłodził dwóch synów.
30 “Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
A gdy się wypełniło czterdzieści lat, ukazał mu się na puszczy góry Synaj Anioł Pański w płomieniu ognistym w krzaku.
31 Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
A Mojżesz ujrzawszy, zadziwił się onemu widzeniu; a gdy przystąpił, aby się temu przypatrzył, stał się do niego głos Pański:
32 ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
Jam jest Bóg ojców twoich, Bóg Abrahama, Bóg Izaaka, i Bóg Jakóba. A zadrżawszy Mojżesz nie śmiał się przypatrywać.
33 “Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
I rzekł mu Pan: Zzuj obuwie z nóg twoich; bo miejsce, na którem stoisz, jest ziemia święta.
34 Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
Widząc widziałem utrapienie ludu mego, który jest w Egipcie, i słyszałem wzdychanie ich, a zstąpiłem, żebym je wybawił; przetoż teraz chodź, poślę cię do Egiptu.
35 “Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
Tego Mojżesza, którego się byli zaprzali, mówiąc: Któż cię postanowił książęciem i sędzią? Tego Bóg książęciem i wybawicielem posłał przez rękę Anioła, który mu się ukazał w krzaku.
36 Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
I ten je wywiódł, czyniąc cuda i znamiona w ziemi Egipskiej i na morzu Czerwonem, i na puszczy, przez czterdzieści lat.
37 “Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
Tenci jest Mojżesz, który rzekł synom Izraelskim: Proroka wam wzbudzi Pan, Bóg wasz, z braci waszych, jako mię, onego słuchać będziecie;
38 Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
Ten jest, który był w zgromadzeniu na puszczy z Aniołem, który mówił do niego na górze Synaj, i z ojcami naszymi, który przyjął słowa Boże żywe, aby je nam podał.
39 “Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
Któremu nie chcieli posłuszni być ojcowie nasi; ale go odrzucili i obrócili się sercy swemi do Egiptu.
40 Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
Mówiąc do Aarona: Uczyń nam bogi, którzy by szli przed nami; albowiem Mojżeszowi onemu, który nas wywiódł z ziemi Egipskiej, nie wiemy co się stało.
41 A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
I uczynili w one dni cielca i sprawowali ofiarę onemu bałwanowi, i weselili się w sprawach rąk swoich;
42 Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
I odwrócił się Bóg i podał je, aby służyli wojsku niebieskiemu, jako napisano jest w księgach prorockich: Zażeście mu bite i inne ofiary ofiarowali na puszczy przez czterdzieści lat, domu Izraelski?
43 Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
Owszem nosiliście namiot Molocha i gwiazdę boga waszego Remfana, te obrazy, któreście sobie uczynili, abyście się im kłaniali; przetoż was zaprowadzę za Babilon.
44 “Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
Namiot świadectwa mieli ojcowie nasi na puszczy, jako był rozrządził ten, który powiedział Mojżeszowi, aby go uczynił według kształtu, który widział.
45 Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
Który wziąwszy ojcowie nasi, wnieśli z Jozuem tam, gdzie była osiadłość poganów, których Bóg wygnał od obliczności ojców naszych, aż do dni Dawidowych;
46 wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
Który znalazł łaskę przed obliczem Bożem i prosił, aby znalazł namiot Bogu Jakóbowemu.
47 Amma Solomon ne ya gina masa gida.
A Salomon zbudował mu dom.
48 “Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
Ale on Najwyższy nie mieszka w kościołach ręką uczynionych, jako prorok mówi:
49 “‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
Niebo jest stolica moja, a ziemia podnóżek nóg moich. Cóż mi za dom zbudujecie, mówi Pan, albo które jest miejsce odpocznienia mego?
50 Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
Izali ręka moja tego wszystkiego nie uczyniła?
51 “Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
Ludzie twardego karku i nieobrzezanego serca, i uszów! wy się zawżdy sprzeciwiacie Duchowi Świętemu jako ojcowie wasi, tak i wy.
52 An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
Któregoż z proroków nie prześladowali ojcowie wasi, i nie pozabijali tych, którzy przedtem opowiadali o przyjściu tego Sprawiedliwego, któregoście wy się teraz stali zdrajcami i mordercami?
53 ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
Którzyście wzięli zakon przez rozrządzenie anielskie, a nie strzegliście go.
54 Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
Tedy słuchając tego, pukali się w sercach swych i zgrzytali na niego zębami.
55 Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
A on będąc pełen Ducha Świętego, patrząc pilnie w niebo, ujrzał chwałę Bożą i Jezusa stojącego po prawicy Bożej.
56 Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
I rzekł: Oto widzę niebiosa otworzone i Syna człowieczego stojącego po prawicy Bożej.
57 Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
A oni krzyknąwszy głosem wielkim, zatulili uszy swoje i rzucili się na niego jednomyślnie.
58 Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
A wypchnąwszy go z miasta, kamionowali; a świadkowie złożyli szaty swoje u stóp młodzieńca, którego zwano Saul.
59 Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
I kamionowali Szczepana modlącego się i mówiącego: Panie Jezu! przyjmij ducha mojego!
60 Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.
A klęknąwszy na kolana, zawołał głosem wielkim: Panie! nie poczytaj im tego za grzech! A to rzekłszy, zasnął.

< Ayyukan Manzanni 7 >