< Ayyukan Manzanni 7 >
1 Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
«Tout cela est-il vrai?» lui demanda le grand-prêtre.
2 Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
Étienne dit alors: «Mes frères et mes pères, écoutez! Le Dieu de gloire apparut à notre père Abraham, en Mésopotamie, avant son établissement à Charran,
3 Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
et lui dit: «Sors de ton pays et de ta famille et va dans le pays que je te montrerai.»
4 “Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
Il sortit alors du pays des Chaldéens et s'établit à Charran. De là, après la mort de son père, Dieu le fit passer dans ce pays-ci que vous habitez maintenant.»
5 Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
«Il ne lui donna aucune propriété dans ce pays, pas même de quoi poser le pied, mais il promit de le mettre, lui et ses descendants, en sa possession, quoiqu'il n'eût pas d'enfant.
6 Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
Voici comment Dieu parla: «Ses descendants demeureront dans un pays étranger, on les fera esclaves et on les persécutera pendant quatre cents ans
7 Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
et la nation qui les fera esclaves c'est moi qui la jugerai, dit Dieu, et ensuite ils partiront et me rendront un culte dans ce lieu-ci.»
8 Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
«Puis Dieu fit avec Abraham l'alliance de la circoncision. C'est ainsi qu'ayant engendré Isaac, Abraham le circoncit le huitième jour, de même Isaac Jacob, et Jacob les douze patriarches.»
9 “Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
«Les patriarches, jaloux de Joseph, le vendirent pour le faire emmener en Égypte.»
10 ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
«Mais Dieu était avec lui, il le tira de toutes ses épreuves, il lui donna de la sagesse et lui fit trouver grâce devant Pharaon, roi d'Égypte, qui l'établit gouverneur d'Égypte et de toute sa maison.»
11 “Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
«Il survint une famine dans toute l'Égypte et en Chanaan, la détresse était grande, et nos pères ne trouvaient pas de quoi se nourrir.
12 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
Mais Jacob apprit qu'il y avait du blé en Égypte et il y envoya nos pères une première fois.
13 A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
Au second voyage, Joseph se fit reconnaître par ses frères et Pharaon apprit quelle était l'origine de Joseph.»
14 Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
«Alors Joseph envoya chercher son père Jacob et toute sa famille, en tout soixante-quinze personnes.
15 Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
Jacob descendit en Égypte et y mourut; nos pères aussi;
16 Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
on les transporta à Sichem et on les déposa dans le tombeau qu'Abraham, à prix d'argent, y avait acheté des fils d'Emmor.»
17 “Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
«Lorsque approcha le moment où devait s'accomplir la promesse solennellement faite par Dieu à Abraham, le peuple s'accrut et se multiplia en Égypte
18 Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
jusqu'au règne d'un autre roi qui n'avait pas connu Joseph.»
19 Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
Celui-ci traita notre peuple par la ruse et persécuta nos pères jusqu'à leur faire exposer leurs enfants pour leur ôter la vie.»
20 “A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
«C'est alors que naquit Moïse; il était d'une divine beauté; trois mois il fut élevé dans la maison de son père.
21 Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
Quand il fut exposé, la fille de Pharaon le recueillit et l'éleva comme son propre fils.
22 Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
Moïse fut instruit dans toute la sagesse des Égyptiens; il était puissant en paroles et en oeuvres.»
23 “Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
«Quand il eut quarante ans accomplis, il lui monta au coeur le désir de visiter ses frères les enfants d'Israël.
24 Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
Il en vit maltraiter un et, prenant son parti, il vengea le tort qui lui était fait en frappant l'Égyptien.
25 Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
Il pensait faire comprendre à ses frères que Dieu, par ses mains, voulait les délivrer; mais ils ne comprirent pas.
26 Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
Le lendemain il se présenta à eux pendant qu'ils se querellaient et comme il les exhortait à se réconcilier en leur disant: «Vous êtes frères, pourquoi vous maltraitez-vous?»
27 “Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
celui qui faisait tort à son prochain le repoussa par ces mots: «Qui donc t'a nommé notre chef et notre juge?
28 Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
Voudrais-tu me tuer, moi aussi, comme l'Égyptien que tu as tué hier?»
29 Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
A cette parole, Moïse prit la fuite et alla vivre en étranger dans le pays de Madian, où il engendra deux fils.»
30 “Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
«Quarante ans plus tard, un ange lui apparut au désert du mont Sinaï dans la flamme d'un buisson en feu.
31 Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
Moïse le vit et, tout surpris de cette apparition, il s'approchait pour la considérer de plus près, lorsque la voix du Seigneur se fit entendre:
32 ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
«Je suis le Dieu de tes pères, le Dieu d'Abraham et d'Isaac et de Jacob.
33 “Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
Tremblant de peur, Moïse n'osa pas regarder davantage. Alors le Seigneur lui dit: «Ote de tes pieds tes chaussures, car le lieu où tu te trouves est une terre sainte;
34 Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
j'ai regardé et j'ai vu la misère de mon peuple en Égypte, et j'ai entendu ses gémissements et je suis descendu pour le délivrer. Viens maintenant pour que je t'envoie en Égypte.»
35 “Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
«C'est ce Moïse qu'ils avaient renié en disant: «Qui donc t'a nommé notre chef et notre juges?» que Dieu a envoyé comme chef et comme libérateur avec l'aide de l'ange qui lui était apparu dans le buisson.
36 Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
C'est lui qui les a délivrés en faisant des prodiges et des miracles en Égypte, sur la mer Rouge et au désert pendant quarante ans.
37 “Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
C'est ce Moïse qui a dit aux enfants d'Israël: «Dieu vous suscitera d'entre vos frères un prophète semblable à moi.»
38 Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
C'est lui qui était au milieu de l'assemblée au désert avec l'ange qui lui parlait sur le mont Sinaï et avec nos pères. C'est lui qui reçut, pour vous les transmettre, des oracles de vie.
39 “Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
C'est à lui que nos pères n'ont pas voulu obéir. C'est lui qu'ils repoussèrent pour tourner leurs coeurs vers l'Égypte,
40 Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
disant à Aaron: «Fais-nous des dieux qui nous conduisent; car ce Moïse, qui nous a fait sortir du pays d'Égypte, nous ne savons ce qui lui est arrivé.»
41 A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
«En ces jours-là, ils fabriquèrent un veau et ils offrirent un sacrifice à cette idole et célébrèrent une joyeuse fête à ces oeuvres de leurs mains.
42 Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
Alors Dieu les abandonna et les livra au culte de l'armée du ciel, comme il est écrit dans le livre des Prophètes: «M'avez-vous offert des victimes et des sacrifices Au désert pendant quarante ans, ô maison d' Israël,
43 Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
Quand vous transportiez le tabernacle de Moloch et l'étoile de votre dieu Romphan, Ces idoles que vous avez fabriquées pour vous prosterner devant elles? Eh bien, je vous déporterai au delà de Babylone.»
44 “Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
«Nos pères avaient au désert le tabernacle du témoignage, comme l'avait ordonné celui qui avait dit à Moïse de le faire sur le modèle qu'il avait vu.
45 Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
Nos pères, l'ayant reçu à leur tour, l'introduisirent avec Josué dans le pays conquis sur les peuples chassés par Dieu devant eux. Il en fut ainsi jusqu'au jour de David
46 wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
qui trouva grâce devant Dieu et demanda à élever une demeure à la maison de Jacob.
47 Amma Solomon ne ya gina masa gida.
Ce fut Salomon qui lui bâtit une maison.»
48 “Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
«Mais le Très Haut n'habite point dans ce qui est fait de mains d'hommes, comme le dit le prophète:
49 “‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
«Le ciel est mon trône, La terre est mon marchepied; Quelle maison m'édifierez-vous, dit le Seigneur, Ou quel sera mon lieu de repos?
50 Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
N'est-ce pas ma main qui a fait toutes ces choses?»
51 “Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
«Têtes dures! coeurs et oreilles incirconcis! vous résistez toujours à l'Esprit saint, comme l'ont fait vos pères!
52 An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
Lequel des prophètes vos pères n'ont-ils pas persécuté! Ils ont tué ceux qui annonçaient la venue du Juste, que vous avez trahi et dont vous avez été les meurtriers!
53 ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
Cette Loi que vous aviez reçue sur les ordres des anges, vous ne l'avez pas gardée...»
54 Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
Ces paroles leur mirent la rage au coeur et ils grincèrent des dents contre Étienne;
55 Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
mais lui, plein d'Esprit saint, les yeux fixés au ciel, vit la gloire de Dieu et Jésus debout à la droite de Dieu,
56 Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
et il dit: «Voilà que je vois les cieux ouverts et le Fils de l'homme debout à la droite de Dieu!»
57 Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
Alors ils poussèrent de grands cris, se bouchèrent les oreilles, se précipitèrent tous ensemble sur lui
58 Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
et l'entraînèrent hors de la ville, où ils le lapidèrent. Les témoins déposèrent leurs vêtements aux pieds d'un jeune homme nommé Saul
59 Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
et, pendant qu'ils le lapidaient, Étienne priait et disait: «Seigneur Jésus, reçois mon esprit.»
60 Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.
Puis il se mit à genoux et s'écria à haute voix: «Seigneur ne leur demande pas compte de ce péché!» En prononçant les paroles, il s'endormit.