< Ayyukan Manzanni 7 >
1 Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
And the chief priest said, 'Are then these things so?'
2 Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
and he said, 'Men, brethren, and fathers, hearken: The God of the glory did appear to our father Abraham, being in Mesopotamia, before his dwelling in Haran,
3 Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
and He said to him, Go forth out of thy land, and out of thy kindred, and come to a land that I shall shew thee.
4 “Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
'Then having come forth out of the land of the Chaldeans, he dwelt in Haran, and from thence, after the death of his father, He did remove him to this land wherein ye now dwell,
5 Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
and He gave him no inheritance in it, not even a footstep, and did promise to give it to him for a possession, and to his seed after him — he having no child.
6 Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
'And God spake thus, That his seed shall be sojourning in a strange land, and they shall cause it to serve, and shall do it evil four hundred years,
7 Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
and the nation whom they shall serve I will judge, said God; and after these things they shall come forth and shall do Me service in this place.
8 Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
'And He gave to him a covenant of circumcision, and so he begat Isaac, and did circumcise him on the eighth day, and Isaac [begat] Jacob, and Jacob — the twelve patriarchs;
9 “Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
and the patriarchs, having been moved with jealousy, sold Joseph to Egypt, and God was with him,
10 ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
and did deliver him out of all his tribulations, and gave him favour and wisdom before Pharaoh king of Egypt, and he did set him — governor over Egypt and all his house.
11 “Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
'And there came a dearth upon all the land of Egypt and Canaan, and great tribulation, and our fathers were not finding sustenance,
12 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
and Jacob having heard that there was corn in Egypt, sent forth our fathers a first time;
13 A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
and at the second time was Joseph made known to his brethren, and Joseph's kindred became manifest to Pharaoh,
14 Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
and Joseph having sent, did call for his father Jacob, and all his kindred — with seventy and five souls —
15 Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
and Jacob went down to Egypt, and died, himself and our fathers,
16 Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
and they were carried over into Sychem, and were laid in the tomb that Abraham bought for a price in money from the sons of Emmor, of Sychem.
17 “Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
'And according as the time of the promise was drawing nigh, which God did swear to Abraham, the people increased and multiplied in Egypt,
18 Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
till another king rose, who had not known Joseph;
19 Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
this one, having dealt subtilely with our kindred, did evil to our fathers, causing to expose their babes, that they might not live;
20 “A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
in which time Moses was born, and he was fair to God, and he was brought up three months in the house of his father;
21 Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
and he having been exposed, the daughter of Pharaoh took him up, and did rear him to herself for a son;
22 Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
and Moses was taught in all wisdom of the Egyptians, and he was powerful in words and in works.
23 “Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
'And when forty years were fulfilled to him, it came upon his heart to look after his brethren, the sons of Israel;
24 Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
and having seen a certain one suffering injustice, he did defend, and did justice to the oppressed, having smitten the Egyptian;
25 Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
and he was supposing his brethren to understand that God through his hand doth give salvation; and they did not understand.
26 Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
'On the succeeding day, also, he shewed himself to them as they are striving, and urged them to peace, saying, Men, brethren are ye, wherefore do ye injustice to one another?
27 “Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
and he who is doing injustice to the neighbour, did thrust him away, saying, Who set thee a ruler and a judge over us?
28 Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
to kill me dost thou wish, as thou didst kill yesterday the Egyptian?
29 Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
'And Moses fled at this word, and became a sojourner in the land of Midian, where he begat two sons,
30 “Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
and forty years having been fulfilled, there appeared to him in the wilderness of mount Sinai a messenger of the Lord, in a flame of fire of a bush,
31 Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
and Moses having seen did wonder at the sight; and he drawing near to behold, there came a voice of the Lord unto him,
32 ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
I [am] the God of thy fathers; the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob. 'And Moses having become terrified, durst not behold,
33 “Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
and the Lord said to him, Loose the sandal of thy feet, for the place in which thou hast stood is holy ground;
34 Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
seeing I have seen the affliction of My people that [is] in Egypt, and their groaning I did hear, and came down to deliver them; and now come, I will send thee to Egypt.
35 “Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
'This Moses, whom they did refuse, saying, Who did set thee a ruler and a judge? this one God a ruler and a redeemer did send, in the hand of a messenger who appeared to him in the bush;
36 Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
this one did bring them forth, having done wonders and signs in the land of Egypt, and in the Red Sea, and in the wilderness forty years;
37 “Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
this is the Moses who did say to the sons of Israel: A prophet to you shall the Lord your God raise up out of your brethren, like to me, him shall ye hear.
38 Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
'This is he who was in the assembly in the wilderness, with the messenger who is speaking to him in the mount Sinai, and with our fathers who did receive the living oracles to give to us;
39 “Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
to whom our fathers did not wish to become obedient, but did thrust away, and turned back in their hearts to Egypt,
40 Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
saying to Aaron, Make to us gods who shall go on before us, for this Moses, who brought us forth out of the land of Egypt, we have not known what hath happened to him.
41 A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
'And they made a calf in those days, and brought a sacrifice to the idol, and were rejoicing in the works of their hands,
42 Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
and God did turn, and did give them up to do service to the host of the heaven, according as it hath been written in the scroll of the prophets: Slain beasts and sacrifices did ye offer to Me forty years in the wilderness, O house of Israel?
43 Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
and ye took up the tabernacle of Moloch, and the star of your god Remphan — the figures that ye made to bow before them, and I will remove your dwelling beyond Babylon.
44 “Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
'The tabernacle of the testimony was among our fathers in the wilderness, according as He did direct, who is speaking to Moses, to make it according to the figure that he had seen;
45 Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
which also our fathers having in succession received, did bring in with Joshua, into the possession of the nations whom God did drive out from the presence of our fathers, till the days of David,
46 wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
who found favour before God, and requested to find a tabernacle for the God of Jacob;
47 Amma Solomon ne ya gina masa gida.
and Solomon built Him an house.
48 “Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
'But the Most High in sanctuaries made with hands doth not dwell, according as the prophet saith:
49 “‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
The heaven [is] My throne, and the earth My footstool; what house will ye build to Me? saith the Lord, or what [is] the place of My rest?
50 Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
hath not My hand made all these things?
51 “Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
'Ye stiff-necked and uncircumcised in heart and in ears! ye do always the Holy Spirit resist; as your fathers — also ye;
52 An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
which of the prophets did not your fathers persecute? and they killed those who declared before about the coming of the Righteous One, of whom now ye betrayers and murderers have become,
53 ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
who received the law by arrangement of messengers, and did not keep [it].'
54 Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
And hearing these things, they were cut to the hearts, and did gnash the teeth at him;
55 Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
and being full of the Holy Spirit, having looked stedfastly to the heaven, he saw the glory of God, and Jesus standing on the right hand of God,
56 Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
and he said, 'Lo, I see the heavens having been opened, and the Son of Man standing on the right hand of God.'
57 Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
And they, having cried out with a loud voice, stopped their ears, and did rush with one accord upon him,
58 Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
and having cast him forth outside of the city, they were stoning [him] — and the witnesses did put down their garments at the feet of a young man called Saul —
59 Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
and they were stoning Stephen, calling and saying, 'Lord Jesus, receive my spirit;'
60 Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.
and having bowed the knees, he cried with a loud voice, 'Lord, mayest thou not lay to them this sin;' and this having said, he fell asleep.