< Ayyukan Manzanni 7 >
1 Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
Then the High Priest asked him, "Are these statements true?"
2 Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
The reply of Stephen was, "Sirs--brethren and fathers--listen to me. God Most Glorious appeared to our forefather Abraham when he was living in Mesopotamia, before he settled in Haran,
3 Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
and said to him, "'Leave your country and your relatives, and go into whatever land I point out to you.'
4 “Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
"Thereupon he left Chaldaea and settled in Haran till after the death of his father, when God caused him to remove into this country where you now live.
5 Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
But he gave him no inheritance in it, no, not a single square yard of ground. And yet He promised to bestow the land as a permanent possession on him and his posterity after him--and promised this at a time when Abraham was childless.
6 Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
And God declared that Abraham's posterity should for four hundred years make their home in a country not their own, and be reduced to slavery and be oppressed.
7 Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
"'And the nation, whichever it is, that enslaves them, I will judge,' said God; 'and afterwards they shall come out, and they shall worship Me in this place.'
8 Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
"Then He gave him the Covenant of circumcision, and under this Covenant he became the father of Isaac--whom he circumcised on the eighth day. Isaac became the father of Jacob, and Jacob became the father of the twelve Patriarchs.
9 “Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
"The Patriarchs were jealous of Joseph and sold him into slavery in Egypt. But God was with him
10 ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
and delivered him from all his afflictions, and gave him favour and wisdom when he stood before Pharaoh, king of Egypt, who appointed him governor over Egypt and all the royal household.
11 “Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
But there came a famine throughout the whole of Egypt and Canaan--and great distress--so that our forefathers could find no food.
12 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
When, however, Jacob heard that there was wheat to be had, he sent our forefathers into Egypt; that was the first time.
13 A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
On their second visit Joseph made himself known to his brothers, and Pharaoh was informed of Joseph's parentage.
14 Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
Then Joseph sent and invited his father Jacob and all his family, numbering seventy-five persons, to come to him,
15 Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
and Jacob went down into Egypt. There he died, and so did our forefathers,
16 Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
and they were taken to Shechem and were laid in the tomb which Abraham had bought from the sons of Hamor at Shechem for a sum of money paid in silver.
17 “Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
"But as the time drew near for the fulfilment of the promise which God had made to Abraham, the people became many times more numerous in Egypt,
18 Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
until there arose a foreign king over Egypt who knew nothing of Joseph.
19 Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
He adopted a crafty policy towards our race, and oppressed our forefathers, making them cast out their infants so that they might not be permitted to live.
20 “A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
At this time Moses was born--a wonderfully beautiful child; and for three months he was cared for in his father's house.
21 Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
At length he was cast out, but Pharaoh's daughter adopted him, and brought him up as her own son.
22 Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
So Moses was educated in all the learning of the Egyptians, and possessed great influence through his eloquence and his achievements.
23 “Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
"And when he was just forty years old, it occurred to him to visit his brethren the descendants of Israel.
24 Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
Seeing one of them wrongfully treated he took his part, and secured justice for the ill-treated man by striking down the Egyptian.
25 Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
He supposed his brethren to be aware that by him God was sending them deliverance; this, however, they did not understand.
26 Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
The next day, also, he came and found two of them fighting, and he endeavoured to make peace between them. "'Sirs,' he said, 'you are brothers. Why are you wronging one another?'
27 “Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
"But the man who was doing the wrong resented his interference, and asked, "'Who appointed you magistrate and judge over us?
28 Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
Do you mean to kill me as you killed the Egyptian yesterday?'
29 Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
"Alarmed at this question, Moses fled from the country and went to live in the land of Midian. There he became the father of two sons.
30 “Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
"But at the end of forty years there appeared to him in the Desert of Mount Sinai an angel in the middle of a flame of fire in a bush.
31 Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
When Moses saw this he wondered at the sight; but on his going up to look further, the voice of the Lord was heard, saying,
32 ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
"'I am the God of your forefathers, the God of Abraham, of Isaac, and of Jacob.' "Quaking with fear Moses did not dare gaze.
33 “Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
"'Take off your shoes,' said the Lord, 'for the spot on which you are standing is holy ground.
34 Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
I have seen, yes, I have seen the oppression of My people who are in Egypt and have heard their groans, and I have come down to deliver them. And now I will send you to Egypt.'
35 “Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
"The Moses whom they rejected, asking him, 'Who appointed you magistrate and judge?' --that same Moses we find God sending as a magistrate and a deliverer by the help of the angel who appeared to him in the bush.
36 Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
This was he who brought them out, after performing marvels and signs in Egypt and at the Red Sea, and in the Desert for forty years.
37 “Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
This is the Moses who said to the descendants of Israel, "'God will raise up a Prophet for you, from among your brethren, just as He raised me up.'
38 Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
'This is he who was among the Congregation in the Desert, together with the angel who spoke to him on Mount Sinai and with our forefathers, who received ever-living utterances to hand on to us.
39 “Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
"Our forefathers, however, would not submit to him, but spurned his authority and in their hearts turned back to Egypt.
40 Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
They said to Aaron, "'Make gods for us, to march in front of us; for as for this Moses who brought us out of the land of Egypt, we do not know what has become of him.'
41 A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
"Moreover they made a calf at that time, and offered a sacrifice to the idol and kept rejoicing in the gods which their own hands had made.
42 Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
So God turned from them and gave them up to the worship of the Host of Heaven, as it is written in the Book of the Prophets, "'Were they victims and sacrifices which you offered Me, forty years in the Desert, O House of Israel?
43 Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
Yes, you lifted up Moloch's tent and the Star of the God Rephan--the images which you made in order to worship them; and I will remove you beyond Babylon.'
44 “Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
"Our forefathers had the Tent of the Testimony in the Desert, built as He who spoke to Moses had instructed him to make it in imitation of the model which he had seen.
45 Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
That Tent was bequeathed to the next generation of our forefathers. Under Joshua they brought it with them when they were taking possession of the land of the Gentile nations, whom God drove out before them. So it continued till David's time.
46 wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
David obtained favour with God, and asked leave to provide a dwelling-place for the God of Jacob.
47 Amma Solomon ne ya gina masa gida.
But it was Solomon who built a house for Him.
48 “Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
Yet the Most High does not dwell in buildings erected by men's hands. But, as the Prophet declares,
49 “‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
"'The sky is My throne, and earth is the footstool for My feet. What kind of house will you build for Me, says the Lord, or what resting place shall I have?
50 Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
Did not My hand form this universe.'
51 “Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
"O stiff-necked men, uncircumcised in heart and ears, you also are continually at strife with the Holy Spirit--just as your forefathers were.
52 An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
Which of the Prophets did not your forefathers persecute? Yes, they killed those who announced beforehand the advent of the righteous One, whose betrayers and murderers you have now become--
53 ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
you who received the Law given through angels, and yet have not obeyed it."
54 Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
As they listened to these words, they became infuriated and gnashed their teeth at him.
55 Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
But, full of the Holy Spirit and looking up to Heaven, Stephen saw the glory of God, and Jesus standing at God's right hand.
56 Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
"I can see Heaven wide open," he said, "and the Son of Man standing at God's right hand."
57 Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
Upon this, with a loud outcry they stopped their ears, rushed upon Stephen in a body,
58 Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
dragged him out of the city, and stoned him, the witnesses throwing off their outer garments and giving them into the care of a young man called Saul.
59 Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
So they stoned Stephen, while he prayed, "Lord Jesus, receive my spirit."
60 Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.
Then, rising on his knees, he cried aloud, "Lord, do not reckon this sin against them." And with these words he fell asleep.