< Ayyukan Manzanni 7 >
1 Sai babban firist ya tambaye shi ya ce, “Waɗannan zargen gaskiya ne?”
Bangʼe jadolo maduongʼ nopenjo Stefano niya, “Weche modonjnigogi bende gin adier?”
2 Game da wannan ya amsa ya ce, “’Yan’uwa da ubanni, ku saurare ni! Allah mai ɗaukaka ya bayyana ga kakanmu Ibrahim yayinda yake a ƙasar Mesofotamiya tukuna, kafin ya yi zama a Haran.
Stefano nodwoko niya, “Owetena kod wuonena, winjauru! Nyasaye man-gi duongʼ maber nofwenyore ni wuonwa Ibrahim kane pod odak e piny Mesopotamia, kane pok odar odhi odak Haran.
3 Allah ya ce, ‘Ka bar ƙasarka da kuma mutanenka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.’
Nyasaye nowachone ni, ‘Dar iwe pinyu gi jou mondo idhi e piny ma abiro nyisi!’
4 “Saboda haka ya bar ƙasar Kaldiyawa ya kuma yi zama a Haran. Bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya aika da shi wannan ƙasar da yanzu kuke zama.
“Omiyo Ibrahim nodar oweyo piny jo-Kaldea mi odhi odak e piny Haran. Bangʼ tho wuon-gi, Nyasaye nooro Ibrahim e piny makoro udakieni.
5 Bai ba shi gādo a nan ba, ko taki ɗaya na ƙasa. Amma Allah ya yi masa alkawari cewa shi da zuriyarsa masu zuwa bayansa za su mallaki ƙasar, ko da yake a lokacin Ibrahim ba shi da yaro.
To ne ok omiye girkeni moro e pinyni, kata lowo matin moromo tielo nyono. Nyasaye nosingorene ni en kaachiel gi nyikwaye mane biro aa bangʼe ne biro kawo lopni, kata obedo ni Ibrahim ne onge gi nyathi e kindeno.
6 Allah ya yi magana da shi ta haka, ‘Shekara ɗari huɗu, zuriyarka za tă yi baƙunci a wata ƙasar da ba tasu ba, za su yi bauta su kuma sha wulaƙanci.
Nyasaye nowuoyo kode kawacho ni, ‘Nyikwayi nobed jodak e piny moro ma ok margi, kendo nolokgi wasumbini mi nosandgi malit kuom higni mia angʼwen.
7 Amma zan hore ƙasar da suka bauta wa.’ Allah ya ce, ‘Kuma daga baya za su fita daga wannan ƙasa su kuma yi mini sujada a wannan wuri.’
To anakum piny ma noketgi wasumbini, bangʼe giniwuogi gia e pinyno mi gibi gilama kae.’
8 Sa’an nan ya yi wa Ibrahim alkawari game da kaciya. Ibrahim kuwa ya zama mahaifin Ishaku ya kuma yi masa kaciya kwana takwas bayan haihuwarsa. Daga baya Ishaku ya zama mahaifin Yaƙub, Yaƙub kuma ya zama mahaifin kakanninmu sha biyun nan.
Bangʼe Nyasaye notimo gi Ibrahim singruok kowacho ni yawuowi nyaka ter nyangu. Kane Ibrahim onywolo wuode ma Isaka, notere nyangu bangʼ ndalo aboro kosenywole. Achien Isaka nonywolo Jakobo, kendo Jakobo bende nodoko wuon kwerewa apar gariyo.
9 “Domin kakanninmu sun ji kishin Yusuf, sai suka sayar da shi bawa zuwa Masar. Amma Allah ya kasance tare da shi
“Nikech kwerewago ne nyiego omako gi Josef, ne giuse kaka misumba ne jo-Misri. To nikech Nyasaye ne ni kode,
10 ya kuma cece shi daga dukan wahalolinsa. Ya ba wa Yusuf hikima ya kuma sa ya sami farin jini a wurin Fir’auna, sarkin Masar; saboda haka ya mai da shi mai mulki a kan Masar da kuma dukan fadarsa.
nokonye e chandruok duto mane oyudo. Ne omiyo Josef rieko ma kinde gi Farao ruodh Misri obedo maber. Omiyo Farao nokete jatelo maduongʼ morito piny Misri duto, nyaka od ruoth bende.
11 “Sai yunwa ta auko wa dukan Masar da Kan’ana, ta kawo wahala mai tsanani, kakanninmu ba su iya samun abinci ba.
“Eka kech maduongʼ nomako piny Misri gi Kanaan kendo nokelo chandruok maduongʼ e piny ma kata kwerewa ne ok nyal yudo chiemo.
12 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa akwai hatsi a Masar, sai ya aiki kakanninmu ziyararsu ta farko.
Kane Jakobo owinjo ni cham ne nitie Misri, nooro kwerewa kuno e ote mokwongo.
13 A ziyararsu ta biyu, Yusuf ya faɗa wa’yan’uwansa wane ne shi, Fir’auna kuwa ya sami sani game da iyalin Yusuf.
To e ote mar ariyo, Josef nohulore ni owetene, mi Farao koro nongʼeyo jo-dalagi Josef.
14 Bayan wannan, Yusuf ya aika a zo da mahaifinsa Yaƙub da dukan iyalinsa, gaba ɗaya dai mutum saba’in da biyar ne.
Bangʼ mano, Josef nooro wach mondo okelne Jakobo wuon mare kaachiel gi wedene duto, mane romo kar kwan ji piero abiriyo gabich.
15 Sai Yaƙub ya gangara zuwa Masar, inda shi da kuma kakanninmu suka mutu.
Kuom mano Jakobo nodhi Misri, kuno ema kwerewa duto kaachiel gi en nothoe.
16 Aka dawo da gawawwakinsu Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya daga wurin’ya’yan Hamor da waɗansu kuɗi a Shekem.
Ringregi ne okel nyaka Shekem mine oyikgi e bur ma Ibrahim nosengʼiewo kuom yawuot Hamor man Shekem.
17 “Da lokaci ya yi kusa da Allah zai cika alkawarin da ya yi wa Ibrahim, sai yawan mutanenmu da suke a Masar ya ƙaru ƙwarai.
“Kane ndalo ochopo mondo Nyasaye ochop singruok mane otimo ni Ibrahim, noyudo ka kar kwan jowa mane odak Misri ne osemedore.
18 Sa’an nan wani sarki, wanda bai san kome game da Yusuf ba, ya zama mai mulkin Masar.
Bangʼe ruoth manyien mane ok ongʼeyo wach Josef nobedo e loch e piny Misri.
19 Ya kuwa wulaƙanta mutanenmu sosai, ya kuma gwada wa kakanni-kakanninmu azaba ta wurin tilasta su su zubar da sababbin jariransu, don su mutu.
Ruodhno nowuondo jowa mosando kwereu malit, ka ochunogi mondo giwit nyithindgi oko mondo otho.
20 “A lokacin nan aka haifi Musa, shi kuwa ba kamar sauran jarirai ba ne. Wata uku aka yi renonsa a gidan mahaifinsa.
“Kindeno ema nonywolie Musa, nyathi mane jaber e nyim Nyasaye kendo nopidhe e od wuon-gi kuom dweche adek.
21 Sa’ad da aka ajiye shi a waje, diyar Fir’auna ta ɗauke shi ta kuma rene shi kamar ɗanta.
To kane owite oko, nyar Farao ne okwanye mi opidhe mana kaka nyathine owuon.
22 Musa ya sami ilimi cikin dukan hikimar Masarawa ya kuma zama mai iko cikin magana da ayyuka.
Musa ne oyudo puonjruok e kit rieko duto mag jo-Misri, kendo ne en ratego e kit wuoyone kod timbene.
23 “Da Musa ya cika shekara arba’in da haihuwa, sai ya yanke shawara yă ziyarci’yan’uwansa Isra’ilawa.
“Kane Musa koro ja-higni piero angʼwen, noparo e chunye mondo odhi olim owetene ma jo-Israel.
24 Ya ga ɗayansu yana shan wulaƙanci a hannun wani mutumin Masar, sai ya je ya kāre shi, ya rama masa ta wurin kashe mutumin Masar ɗin.
Noneno ka ja-Misri moro goyo ja-Israel wadgi, omiyo ne odhi okonye mi nogoyo ja-Misrino monego.
25 Musa ya yi tsammani mutanensa za su gane cewa, Allah yana amfani da shi don yă cece su, amma ba su gane ba.
Musa ne oparo ni owetene ma jo-Israel ne nyalo neno ni Nyasaye ema notiyo kode mondo ogolgi e twech, to ne ok gineno kamano.
26 Kashegari, Musa ya sadu da Isra’ilawa biyu suna faɗa. Ya yi ƙoƙari ya sasanta su, yana cewa, ‘Ku mutane, ku’yan’uwa ne, don me kuke so ku cutar da juna?’
Kinyne Musa noyudo jo-Israel ariyo ka dhawo. Notemo thegogi kowachonegi ni, ‘Joka ma, un owete; angʼo momiyo udwaro hinyoru kayiem?’
27 “Amma mutumin da yake wulaƙanta ɗayan, ya tura Musa a gefe ya ce, ‘Wa ya mai da kai mai mulki, da alƙali a kanmu?
“To ngʼat mane sando nyawadgino nodhiro Musa gichien kowachone ni, ‘En ngʼa ma oketi ruoth kendo jangʼadnwa bura?
28 Kana so ka kashe ni kamar yadda ka kashe mutumin Masar nan na jiya?’
Iparo mar nega kaka nyoro inego ja-Misri cha?’
29 Sa’ad da Musa ya ji haka, sai ya gudu zuwa ƙasar Midiyan, inda ya yi baƙunci, ya kuma haifi’ya’ya biyu maza.
Kane Musa owinjo wachno, noringo odhi Midian, kama nodakie kaka japiny moro mi onywolo yawuowi ariyo.
30 “Bayan shekaru arba’in suka wuce, sai mala’ika ya bayyana ga Musa cikin harshen wuta a ɗan itace a hamada kusa da Dutsen Sinai.
“Bangʼ higni piero angʼwen, malaika nofwenyore ni Musa ei ligek mach maliel e bungu manie thim but Got Sinai.
31 Sa’ad da ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya yi kusa domin ya duba sosai, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,
Kane Musa oneno mach malielno, nodoko maluor. Kane osudo machiegni mondo onene maber, nowinjo dwond Ruoth Nyasaye kawacho niya,
32 ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allah na Ibrahim, Ishaku, da kuma Yaƙub.’ Sai Musa ya yi rawan jiki don tsoro, bai kuwa yi karambanin dubawa ba.
‘An e Nyasach kwereni; ma Nyasach Ibrahim gi Isaka kod Jakobo.’ Omiyo Musa notetni ka luoro omake, kendo ne ok ohedhore ngʼiyo bunguno kendo.
33 “Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, ‘Ka cire takalmanka; wurin da kake tsayen nan mai tsarki ne.
“Eka Ruoth Nyasaye nowachone niya, ‘Lony wuoche e tiendi, nikech kama ichungoeni en Kama Ler!
34 Tabbatacce na ga wulaƙancin da ake yi wa mutanena a Masar. Na ji nishinsu na kuma sauka domin in’yantar da su. Yanzu ka zo, zan aike ka ka koma Masar.’
Aseneno gi wangʼa kaka joga chandore malit e piny Misri. Asewinjo kaka gichur omiyo asebiro mondo agonygi gibed thuolo; koro bi mondo aori idogi Misri!’
35 “Wannan Musa ɗin da suka ƙi suna cewa, ‘Wa ya mai da kai mai mulki da kuma alƙali?’ Allah da kansa ya aike shi, ta wurin mala’ikan da ya bayyana a gare shi a ɗan itace, yă zama mai mulkinsu, da kuma mai cetonsu.
“Ma e Musa mane oyudo gisekwedo kagiwacho ni, ‘En ngʼa ma oketi ruoth kendo jangʼadnwa bura?’ Nyasaye owuon mane ofwenyorene e kit malaika mane oneno e bungu noore mondo obed jatendgi kendo jaresgi.
36 Ya fitar da su daga Masar ya kuma yi ayyukan da abubuwan banmamaki a Masar, a Jan Teku, da kuma cikin hamada har shekara arba’in.
Ne otelonegi kogologi Misri, kendo notimo honni madongo gi ranyisi e piny Misri, e Nam Makwar, kendo timo honni mamoko bende e thim kuom higni piero angʼwen.
37 “Wannan Musa ne ya ce Isra’ilawa, ‘Allah zai aika muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku.’
“Ma e Musa mane onyiso jo-Israel ni, ‘Nyasaye noyiernu janabi machal koda kowuok e dier ogandau.’
38 Ya kasance a cikin taron nan a hamada, tare da mala’ikan da ya yi magana da shi a Dutsen Sinai, da kuma tare da kakanninmu; ya kuma karɓi kalmomi masu rai don yă miƙa mana.
En owuon ne en kodgi e chokruok mane ni e thim, kaachiel gi kwerewa kod malaika mane owuoyo kode e Got Sinai; kendo ne omiye weche mangima makoro wawinjogi.
39 “Amma kakanninmu suka ƙi yin masa biyayya. A maimakon haka, sai suka ƙi shi a cikin zuciyarsu kuwa suka koma Masar.
“To kwerewa notamore winjo wachne. Kar timo mano, to ne gikwede kendo chunygi nogombo dok Misri.
40 Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana allolin da za su yi mana jagora. Game da wannan Musa ɗin wanda ya fitar da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba!’
Neginyiso Harun ni, ‘Losnwa nyiseche moko mondo otelnwa, nikech wakia gima osetimo Musa mane ogolowa Misri!’
41 A lokacin ne suka ƙera gunki mai siffar ɗan maraƙi. Suka kawo masa hadayu suka kuma yi bikin girmama abin da suka ƙera da hannuwansu.
E kindeno ema ne gilosoe kido milamo machalo gi nyaroya. Negitimone misango, mi gilosone sawo ka gimiyo gima lwetgi ema ne oloso duongʼ!
42 Sai Amma Allah ya juya musu baya ya kuma ba da su ga bautar abubuwan da suke a sararin sama. Wannan ya yi daidai da abin da yake a rubuce a cikin littafin annabawa cewa, “‘Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in cikin, hamada, ya gidan Isra’ila?
To Nyasaye nogolo pache kuomgi moweyogi mondo gilam chwech mag polo kaka nyisechegi, mana kaka ondiki e kitap jonabi niya, “‘Yaye jo-Israel, bende ne ukelona misengini kata chiwo moro amora kuom higni piero angʼwen mane un e thim?
43 Kun ɗaukaka gidan tsafin Molek, da tauraron allahnku Refan, gumakan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Saboda haka zan aike ku zuwa bauta’ gaba da Babilon.
Ne utingʼo malo hemb Molek kod sulwe mar nyasachu ma Refan ma gin, nyiseche manono mane uloso mondo ulam. Omiyo abiro darou mi ateru e piny twech mabor mayombo Babulon.’
44 “Kakanni-kakanninmu suna da tabanakul na Shaida tare da su a hamada. An yi shi bisa ga yadda Allah ya umarci Musa, bisa ga zānen da ya gani.
“Kwereu ne ni kod Hema miluongo ni Hemb Rapar. Hemano nolosi mana kaka Nyasaye nonyiso Musa mondo olose, koluwo ranyisi mane omiye.
45 Bayan sun gāji tabanakul nan, kakanninmu a ƙarƙashin jagorancin Yoshuwa suka kawo shi tare da su, lokacin da suka ƙwace ƙasar daga al’umman da Allah ya kora a idanunsu. Tabanakul ɗin ya kasance a ƙasar har zamanin Dawuda,
Kane kwerewa oyudo Hemani, ne gitingʼe ka Joshua otelonegi, nyaka negichopo kode e piny ogendini mane Nyasaye oseriembo mondo owenegi. Hemani ne gibedogo nyaka chop kinde mag Daudi.
46 wanda ya sami tagomashi daga Allah, ya kuma nemi yă yi wa Allah na Yaƙub wurin zama.
Daudi noyudo ngʼwono e wangʼ Nyasaye, omiyo nokwayo mondo ogerne Nyasach Jakobo kar dak.
47 Amma Solomon ne ya gina masa gida.
To Solomon ema ne ogero ne Nyasaye odno.
48 “Duk da haka, Mafi Ɗaukaka ba ya zama a gidajen da mutane suka gina. Kamar yadda annabi ya faɗi cewa,
“Kata kamano, Nyasaye Man Malo Moloyo ok dagi e udi ma dhano ogero, mana kaka janabi owacho niya,
49 “‘Sama ne kursiyina, duniya kuma wurin ajiye tafin ƙafata. Wane irin gida za ka gina mini? Ko kuwa ina wurin hutuna zai kasance? In ji Ubangiji.
“‘Polo e koma mar duongʼ to piny e raten tienda. Koro en ot machal nade ma dugerna? Ruoth Nyasaye owacho. Koso kar yweyo mara nobed kanye?
50 Ba hannuna ne ya yi dukan waɗannan abubuwa ba?’
Donge lweta ema osechweyo gigi duto?’
51 “Ku mutane masu taurinkai, da zukata da kuma kunnuwa marasa kaciya! Kuna kama da kakanninku. Kullum kuna tsayayya da Ruhu Mai Tsarki!
“Un joma tokgi tek, chunyu bor gi Nyasaye kendo udagi winjo wachne! Uchal mana gi kwereu. Usiko utamo Roho Maler tiyo!
52 An yi wani annabin da kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun ma kashe waɗanda suka yi maganar zuwan Mai Adalcin nan. Yanzu kuwa kun bashe shi kuka kuma kashe shi
Bende nitie janabi kata achiel ma kwereu ne ok osando? Neginego nyaka jonabi mane okoro biro mar Ngʼama Kare. To koro usendhoge mi unege.
53 ku da kuka karɓi dokar da aka sa a aiki ta wurin mala’iku amma ba ku yi biyayya da ita ba.”
Un e joma noyudo chik mane okel gi malaike to usetamoru rito chikno.”
54 Da membobin Sanhedrin suka ji haka, sai suka yi fushi suka ciji haƙoransu.
Kane jobura owinjo weche mane Stefano owacho, igi nongʼondore mi gikayone lekegi.
55 Amma Istifanus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dubi sama ya kuma ga ɗaukakar Allah, da Yesu kuma tsaye a hannun dama na Allah.
To Stefano, kopongʼ gi Roho Maler, nongʼiyo malo e polo mi oneno duongʼ mar Nyasaye, kod Yesu kochungʼ e bad Nyasaye korachwich.
56 Ya ce, “Ga shi, na ga sama a buɗe da kuma Ɗan Mutum tsaye a hannun dama na Allah.”
Nowachonegi niya, “Neuru, aneno polo koyawore kendo ka Wuod Dhano ochungʼ e bad Nyasaye korachwich.”
57 Da jin haka sai suka tattoshe kunnuwansu, suka kuma yi ihu da ƙarfi sosai, suka aukar masa gaba ɗaya.
Kane giwinjo wachno, mirima nomakgi matek mi gimwomore kuome gi chuny achiel.
58 Suka ja shi zuwa bayan birnin suka kuma yi ta jifansa da duwatsu. Ana cikin haka, shaidun suka ajiye tufafinsu a wurin wani saurayi mai suna Shawulu.
Ne giywaye mi gigole oko mar dala maduongʼ kendo gichako chiele gi kite. Joneno mag miriambo nohangone wach moketo lepgi e tiend wuowi moro ma nyinge Saulo.
59 Yayinda suke cikin jifansa, sai Istifanus ya yi addu’a ya ce, “Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”
Kane oyudo gichiele gi kite, Stefano nolamo kowacho niya, “Ruoth Yesu, kaw chunya.”
60 Sa’an nan ya durƙusa ya ɗaga murya ya ce, “Ubangiji, kada ka riƙe wannan zunubi a kansu.” Da ya faɗi haka, sai ya yi barci.
Eka nogoyo chonge piny mokok matek niya, “Ruoth, kik ikwan richoni e wigi.” Kane osewacho kamano, to chunye nochot.