< Ayyukan Manzanni 6 >

1 A waɗannan kwanaki, sa’ad da yawan almajirai suke ƙaruwa, sai Yahudawan masu jin Hellenanci a cikinsu suka yi gunaguni a kan Yahudawan da suke Ibraniyawa domin ba a kula da gwaurayensu a wajen raba abinci na yau da kullum.
Vid denna tid, då nu lärjungarnas antal förökades, begynte de grekiska judarna knorra mot de infödda hebréerna över att deras änkor blevo förbisedda vid den dagliga utdelningen.
2 Saboda haka Sha Biyun nan suka tara dukan almajirai wuri ɗaya, suka ce, “Bai zai yi kyau mu bar hidimar maganar Allah don mu shiga hidimar abinci ba.
Då sammankallade de tolv hela lärjungaskaran och sade: »Det är icke tillbörligt att vi försumma Guds ord för att göra tjänst vid borden.
3 ’Yan’uwa, ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku waɗanda aka sani suna cike da Ruhu da kuma hikima. Mu kuwa za mu danƙa musu wannan aiki
Så utsen nu bland eder, I bröder, sju män som hava gott vittnesbörd om sig och äro fulla av ande och vishet, män som vi kunna sätta till att sköta denna syssla.
4 mu kuwa mu mai da halinmu ga yin addu’a da kuma hidimar maganar Allah.”
Vi skola då helt få ägna oss åt bönen och åt ordets tjänst.»
5 Wannan shawarar kuwa ta gamshi dukan ƙungiyar. Sai suka zaɓi Istifanus, mutumin da yake cike da bangaskiya da kuma Ruhu Mai Tsarki; da Filibus, Burokorus, Nikano, Timon, Farmenas, da Nikolas daga Antiyok, wanda ya tuba zuwa Yahudanci.
Det talet behagade hela menigheten. Och de utvalde Stefanus, en man som var full av tro och helig ande, vidare Filippus och Prokorus och Nikanor och Timon och Parmenas, slutligen Nikolaus, en proselyt från Antiokia.
6 Suka gabatar da waɗannan mutane wa manzanni, waɗanda kuwa suka yi addu’a, suka ɗibiya hannuwansu a kansu.
Dem läto de träda fram för apostlarna, och dessa bådo och lade händerna på dem.
7 Saboda haka maganar Allah ta yaɗu. Yawan almajirai a Urushalima kuwa ya yi saurin ƙaruwa, firistoci masu yawa kuma suka zama masu biyayya ga wannan bangaskiya.
Och Guds ord hade framgång, och lärjungarnas antal förökades mycket i Jerusalem; och en stor hop av prästerna blevo lydiga och trodde.
8 To, Istifanus, mutum cike da alheri da ikon Allah, ya aikata manyan ayyukan da alamu masu banmamaki a cikin mutane.
Och Stefanus var full av nåd och kraft och gjorde stora under och tecken bland folket.
9 Sai hamayya ta taso daga’yan ƙungiyar Majami’a na’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus,
Men av dem som hörde till den synagoga som kallades »De frigivnes och cyrenéernas och alexandrinernas synagoga», så ock av dem som voro från Cilicien och provinsen Asien, stodo några upp för att disputera med Stefanus.
10 amma ba su iya cin nasara kan hikimarsa ko kuma a kan Ruhu wanda ta wurinsa ne ya magana ba.
Dock förmådde de icke stå emot den vishet och den ande som här talade.
11 Sa’an nan a asirce suka zuga waɗansu mutane su ce, “Mun ji Istifanus ya faɗa kalmomin saɓo game da Musa da kuma Allah.”
Då skaffade de några män som föregåvo att de hade hört honom tala hädiska ord mot Moses och mot Gud.
12 Ta haka suka tā da hankalin mutane da dattawa da kuma malaman dokoki. Suka kama Istifanus suka kawo shi a gaban Majalisa.
De uppeggade så folket och de äldste och de skriftlärde och överföllo honom och grepo honom och förde honom inför Stora rådet.
13 Suka kawo masu ba da shaidar ƙarya, waɗanda suka ba da shaida cewa, “Wannan mutum ba ya rabuwa da maganar banza a kan wurin nan mai tsarki da kuma doka.
Där läto de falska vittnen träda fram, vilka sade: »Denne man upphör icke att tala mot vår heliga plats och mot lagen.
14 Gama mun ji shi yana cewa wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan ya kuma canja al’adun da Musa ya ba mu.”
Ty vi hava hört honom säga att Jesus, han från Nasaret, skall bryta ned denna byggnad och förändra de stadgar som Moses har givit oss.»
15 Dukan waɗanda suke zaune a Majalisar suka kafa wa Istifanus ido, suka kuma ga fuskarsa ta yi kama da ta mala’ika.
Då nu alla som sutto i Rådet fäste sina ögon på honom, syntes dem hans ansikte vara såsom en ängels ansikte.

< Ayyukan Manzanni 6 >