< Ayyukan Manzanni 6 >

1 A waɗannan kwanaki, sa’ad da yawan almajirai suke ƙaruwa, sai Yahudawan masu jin Hellenanci a cikinsu suka yi gunaguni a kan Yahudawan da suke Ibraniyawa domin ba a kula da gwaurayensu a wajen raba abinci na yau da kullum.
En ce temps-là, comme les disciples se multipliaient, il s'éleva un murmure des Hellénistes contre les Hébreux, parce que leurs veuves étaient négligées dans la distribution qui se faisait chaque jour.
2 Saboda haka Sha Biyun nan suka tara dukan almajirai wuri ɗaya, suka ce, “Bai zai yi kyau mu bar hidimar maganar Allah don mu shiga hidimar abinci ba.
C'est pourquoi les douze, ayant convoqué la multitude des disciples, leur dirent: Il ne convient pas que nous négligions la parole de Dieu, pour le service des tables.
3 ’Yan’uwa, ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku waɗanda aka sani suna cike da Ruhu da kuma hikima. Mu kuwa za mu danƙa musu wannan aiki
Choisissez donc, frères, sept hommes d'entre vous, dont on rende bon témoignage, pleins d'Esprit-Saint et de sagesse, à qui nous commettions cet emploi.
4 mu kuwa mu mai da halinmu ga yin addu’a da kuma hidimar maganar Allah.”
Quant à nous, nous vaquerons à la prière et au ministère de la parole.
5 Wannan shawarar kuwa ta gamshi dukan ƙungiyar. Sai suka zaɓi Istifanus, mutumin da yake cike da bangaskiya da kuma Ruhu Mai Tsarki; da Filibus, Burokorus, Nikano, Timon, Farmenas, da Nikolas daga Antiyok, wanda ya tuba zuwa Yahudanci.
Cette proposition plut à toute l'assemblée; et ils élurent Étienne, homme plein de foi et du Saint-Esprit, et Philippe, et Procore, et Nicanor, et Timon, et Parménas et Nicolas, prosélyte d'Antioche;
6 Suka gabatar da waɗannan mutane wa manzanni, waɗanda kuwa suka yi addu’a, suka ɗibiya hannuwansu a kansu.
Et ils les présentèrent aux apôtres, qui, en priant, leur imposèrent les mains.
7 Saboda haka maganar Allah ta yaɗu. Yawan almajirai a Urushalima kuwa ya yi saurin ƙaruwa, firistoci masu yawa kuma suka zama masu biyayya ga wannan bangaskiya.
Et la parole de Dieu se répandait, et le nombre des disciples se multipliait beaucoup à Jérusalem. Et un grand nombre de sacrificateurs obéissaient à la foi.
8 To, Istifanus, mutum cike da alheri da ikon Allah, ya aikata manyan ayyukan da alamu masu banmamaki a cikin mutane.
Or, Étienne, plein de foi et de puissance, faisait de grands prodiges et de grands miracles parmi le peuple.
9 Sai hamayya ta taso daga’yan ƙungiyar Majami’a na’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus,
Mais quelques personnes de la synagogue, dite des affranchis, et de celles des Cyrénéens, des Alexandrins, et des hommes originaires de Cilicie et d'Asie, se présentèrent pour disputer contre Étienne.
10 amma ba su iya cin nasara kan hikimarsa ko kuma a kan Ruhu wanda ta wurinsa ne ya magana ba.
Et ils ne pouvaient résister à la sagesse et à l'Esprit par lequel il parlait.
11 Sa’an nan a asirce suka zuga waɗansu mutane su ce, “Mun ji Istifanus ya faɗa kalmomin saɓo game da Musa da kuma Allah.”
Alors ils subornèrent des hommes pour dire: Nous lui avons entendu proférer des paroles blasphématoires contre Moïse et contre Dieu.
12 Ta haka suka tā da hankalin mutane da dattawa da kuma malaman dokoki. Suka kama Istifanus suka kawo shi a gaban Majalisa.
Et ils émurent le peuple, et les Anciens, et les Scribes; et se jetant sur lui, ils le saisirent et l'emmenèrent au Sanhédrin;
13 Suka kawo masu ba da shaidar ƙarya, waɗanda suka ba da shaida cewa, “Wannan mutum ba ya rabuwa da maganar banza a kan wurin nan mai tsarki da kuma doka.
Et ils produisirent de faux témoins, qui disaient: Cet homme-ci ne cesse de proférer des paroles blasphématoires contre ce saint lieu et contre la loi.
14 Gama mun ji shi yana cewa wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan ya kuma canja al’adun da Musa ya ba mu.”
Car nous lui avons entendu dire que Jésus, ce Nazarien, détruira ce lieu, et changera les ordonnances que Moïse nous a données.
15 Dukan waɗanda suke zaune a Majalisar suka kafa wa Istifanus ido, suka kuma ga fuskarsa ta yi kama da ta mala’ika.
Et comme tous ceux qui étaient assis dans le Sanhédrin avaient les yeux arrêtés sur lui, son visage leur parut comme celui d'un ange.

< Ayyukan Manzanni 6 >