< Ayyukan Manzanni 5 >
1 To wani mutum mai suna Ananiyas tare da matarsa Saffiratu, shi ma ya sayar da wata mallakarsa.
Or, un homme, nommé Ananias, avec Saphira sa femme, vendit une possession;
2 Da cikakken sanin matarsa ya ajiye sashi daga cikin kuɗin don kansa, ya kuma kawo sauran ya ajiye a sawun manzanni.
Et il retint une part du prix, de concert avec sa femme, et il en apporta le reste, et le mit aux pieds des apôtres.
3 Sai Bitrus ya ce, “Ananiyas, ta yaya Shaiɗan ya cika zuciyarka haka da ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya ka kuma ajiye wa kanka sauran kuɗin da ka karɓa na filin?
Mais Pierre lui dit: Ananias, pourquoi Satan s'est-il emparé de ton cour, que tu aies menti au Saint-Esprit, et détourné une part du prix de la terre?
4 Ba naka ba ne kafin ka sayar da shi? Bayan da ka sayar da shi kuma, kuɗin ba naka ba ne? Me ya sa ka yi tunanin yin irin wannan abu? Ba mutum ne ka yi wa ƙarya ba, Allah ne ka yi masa.”
Si tu l'eusses gardée, ne te demeurait-elle pas? et l'ayant vendue, son prix n'était-il pas en ton pouvoir? Comment as-tu résolu cette action dans ton cour? Ce n'est pas aux hommes que tu as menti, mais à Dieu.
5 Da Ananiyas ya ji wannan, sai ya fāɗi ya mutu. Sai babban tsoro kuwa ya kama duk waɗanda suka ji abin da ya faru.
Ananias, à l'entendue de ces paroles, tomba, et rendit l'esprit; ce qui causa une grande crainte à tous ceux qui en entendirent parler.
6 Sai samari suka zo gaba, suka naɗe gawarsa, suka fitar da shi suka je suka binne.
Et les jeunes gens s'étant levés, le prirent, l'emportèrent, et l'ensevelirent.
7 Bayan kusan awa uku, sai matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba.
Environ trois heures après, sa femme, ne sachant rien de ce qui était arrivé, entra.
8 Bitrus ya tambaye ta ya ce, “Gaya mini, kuɗin da yake da Ananiyas kuka sayar da filin ke nan?” Ta ce, “I, haka ne muka sayar.”
Et Pierre prenant la parole, lui dit: Dis-moi, avez-vous vendu tant le fonds de terre? Et elle dit: Oui, autant.
9 Bitrus ya ce mata, “Ta yaya kuka yarda ku gwada Ruhun Ubangiji? Duba! Sawun mutanen da suka binne mijinki suna bakin ƙofa, za su kuwa ɗauke ki zuwa waje ke ma.”
Alors Pierre lui dit: Pourquoi vous êtes-vous accordés pour tenter l'Esprit du Seigneur? Voilà, ceux qui ont enseveli ton mari sont à la porte, et ils t'emporteront.
10 Nan take ta fāɗi a ƙafafunsa ta mutu. Sai samarin suka shigo ciki, suka kuwa same ta matacciya, suka ɗauke ta suka kai ta waje suka binne ta kusa da mijinta.
Au même instant elle tomba à ses pieds, et expira. Et les jeunes gens, étant entrés, la trouvèrent morte, et l'ayant emportée, ils l'ensevelirent auprès de son mari.
11 Babban tsoro ya kama dukan ikkilisiya da kuma duk wanda ya ji game da abubuwan nan.
Cela donna une grande crainte à toute l'Église, et à tous ceux qui en entendirent parler.
12 Manzannin suka yi ayyukan da alamu masu banmamaki masu yawa a cikin mutanen. Dukan masu bi kuwa sukan taru a Shirayin Solomon.
Or il se faisait beaucoup de miracles et de prodiges parmi le peuple, par le moyen des apôtres; et ils étaient tous d'un commun accord au portique de Salomon.
13 Ba wanda ya yi karambanin shiga cikinsu, duk da haka mutane suna girmama su ƙwarai.
Et aucun des autres n'osait se joindre à eux, mais le peuple leur donnait de grandes louanges.
14 Duk da haka, maza da matan da suke gaskata ga Ubangiji sai ƙaruwa suke, suka kuma ƙaru a yawa.
De plus, des multitudes d'hommes et de femmes, de ceux qui croyaient au Seigneur, étaient ajoutées à l'Église;
15 A sakamakon haka, mutane suka kawo marasa lafiya a tituna suka kwantar da su a kan gadaje da tabarmai domin aƙalla inuwar Bitrus za tă bi kan waɗansunsu yayinda yake wucewa.
En sorte qu'on apportait les malades dans les rues, et on les mettait sur des lits et sur des grabats, afin que quand Pierre viendrait, son ombre du moins couvrît quelques-uns d'entre eux.
16 Jama’a ma suka tattaru daga garuruwa kewaye da Urushalima suna kawo marasa lafiyarsu da kuma waɗanda mugayen ruhohi suke damun su, dukansu kuwa suka warke.
Le peuple des villes voisines venait aussi en foule à Jérusalem; apportant des malades, et des hommes tourmentés par des esprits immondes, et tous étaient guéris.
17 Sai babban firist da dukan abokan aikinsa, waɗanda suke na ƙungiyar Sadukiyawa suka cika da kishi.
Alors, le souverain sacrificateur et tous ceux qui étaient avec lui, lesquels formaient la secte des sadducéens, se levèrent, et furent remplis de jalousie.
18 Suka kama manzannin suka sa su a kurkukun da ake sa kowa da kowa.
Et se saisissant des apôtres, ils les mirent dans la prison publique.
19 Amma da dare wani mala’ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun ya fitar da su.
Mais un ange du Seigneur ouvrit, pendant la nuit, les portes de la prison, et les ayant fait sortir, leur dit:
20 Ya ce, “Ku je ku tsaya a filin haikali ku sanar wa mutane cikakken saƙon wannan sabon rai.”
Allez, et vous tenant dans le temple, annoncez au peuple toutes les paroles de cette vie.
21 Da gari ya waye, sai suka shiga filin haikali, yadda aka faɗa musu, suka kuwa fara koyar da mutane. Sa’ad da babban firist da abokan aikinsa suka iso, sai suka kira Majalisa gaba ɗaya dukan dattawan Isra’ila, suka kuma aika kurkuku a zo da manzannin.
Ayant entendu cela, ils entrèrent, dès le point du jour, dans le temple, et ils y enseignaient. Cependant, le souverain sacrificateur et ceux qui étaient avec lui étant arrivés, ils assemblèrent le Sanhédrin et tout le Conseil des anciens des enfants d'Israël; et ils envoyèrent chercher les apôtres à la prison.
22 Amma da dogarawan suka iso kurkukun, ba su same su a can ba. Saboda haka suka dawo suka ba da labari, suka ce,
Mais quand les sergents y furent allés, ils ne les trouvèrent point dans la prison; et étant revenus,
23 “Mun iske kurkukun a kulle sosai, da masu gadi suna tsaye a bakin ƙofofin; amma da muka buɗe su, sai muka tarar ba kowa a ciki.”
Ils l'annoncèrent en disant: Nous avons trouvé la prison fermée en toute sûreté et les gardes en sentinelle dehors devant les portes; mais l'ayant ouverte, nous n'avons trouvé personne dedans.
24 Da jin wannan labari, sai shugaban masu gadin haikali da manyan firistocin suka ruɗe, suna tunanin abin da wannan al’amari zai zama.
Le souverain sacrificateur, le capitaine du temple et les principaux sacrificateurs, ayant entendu cela, ne savaient que penser au sujet des apôtres, de ce qui en arriverait.
25 Sai wani ya zo ya ce, “Ga shi! Mutanen da kuka sa a kurkuku suna tsaye a filin haikali suna koya wa mutane.”
Mais quelqu'un survint, qui leur fit ce rapport: Voici, les hommes que vous avez mis en prison, sont dans le temple, et enseignent le peuple.
26 Da wannan, shugaban ya tafi tare da dogarawansa suka kawo manzannin. Sun kawo su amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada mutane su jajjefe su da duwatsu.
Alors le capitaine s'en alla avec les huissiers, et les amena sans violence; car ils craignaient d'être lapidés par le peuple.
27 Da suka kawo manzannin, sai suka sa su suka bayyana a gaban Majalisar don babban firist ya tuhume su.
Et les ayant amenés, ils les présentèrent au Sanhédrin. Et le souverain sacrificateur les interrogea, en disant:
28 Ya ce, “Mun kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa cikin wannan suna, duk da haka kun cika Urushalima da koyarwarku, har ma kuna so ku ɗora mana laifin jinin mutumin nan.”
Ne vous avons-nous pas défendu expressément d'enseigner en ce nom-là? Et vous avez rempli Jérusalem de votre doctrine, et vous voulez faire retomber sur nous le sang de cet homme.
29 Bitrus da sauran manzannin suka amsa suka ce, “Dole ne mu yi wa Allah biyayya a maimakon mutane!
Mais Pierre et les apôtres répondirent: Il faut obéir à Dieu plutôt qu'aux hommes.
30 Allahn kakanninmu ya tā da Yesu daga matattu, wanda kuka kashe ta wurin ratayewa a bisan itace.
Le Dieu de nos pères a ressuscité Jésus, que vous avez fait mourir, en le pendant au bois.
31 Allah ya ɗaukaka shi zuwa hannun damansa a matsayin Yerima da Mai Ceto don yă kawo tuba da gafarar zunubai ga Isra’ila.
Dieu l'a élevé à sa droite, comme le Prince et Sauveur, afin de donner à Israël la repentance et la rémission des péchés.
32 Mu shaidu ne ga waɗannan abubuwa, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya ba wa waɗanda suke yin masa biyayya.”
Et nous lui sommes témoins de ces choses, aussi bien que le Saint-Esprit, que Dieu a donné à ceux qui lui obéissent.
33 Da suka ji haka, sai suka yi fushi suka so su kashe su.
Eux entendant cela, grinçaient des dents, et ils délibéraient de les faire mourir.
34 Amma wani Bafarisiyen da ake kira Gamaliyel, wani malamin doka, wanda dukan mutane ke girmamawa, ya miƙe tsaye a Majalisar ya umarta a fitar da mutanen waje na ɗan lokaci.
Mais un Pharisien, nommé Gamaliel, docteur de la loi, honoré de tout le peuple, se levant dans le Sanhédrin, commanda qu'on fît retirer les apôtres pour un peu de temps.
35 Sa’an nan ya yi musu jawabi ya ce, “Mutanen Isra’ila, ku yi kula da kyau da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan.
Et il leur dit: Hommes Israélites, prenez garde à ce que vous avez à faire à l'égard de ces gens.
36 Kwanan baya, Teyudas ya ɓullo, yana cewa wai shi wani mutum ne, kuma wajen mutane ɗari huɗu suka bi shi. Aka kuwa kashe shi, dukan masu binsa kuwa suka watse, kome ya wargaje.
Car, il y a quelque temps que Theudas s'éleva, se disant être quelque chose; auquel un nombre d'environ quatre cents hommes se joignit; mais il fut tué, et tous ceux qui l'avaient cru furent dispersés et réduits à rien.
37 Bayansa, Yahuda mutumin Galili ya ɓullo a kwanakin ƙidaya, ya jagoranci mutane cikin tawaye. Shi ma aka kashe shi, dukan mabiyansa kuma aka watsar da su.
Après lui, au temps du dénombrement, s'éleva Judas le Galiléen, qui attira à lui un grand peuple; mais il périt aussi, et tous ceux qui le crurent furent dispersés.
38 Saboda haka, a wannan batu na yanzu, ina ba ku shawara. Ku ƙyale mutanen nan! Ku bar su su tafi! Gama in manufarsu ko ayyukansu na mutum ne, ai, zai rushe.
Je vous dis donc maintenant: Ne poursuivez point ces gens-là, et laissez-les aller; car si cette entreprise ou cette ouvre vient des hommes, elle sera détruite;
39 Amma in daga Allah ne, ba za ku iya hana waɗannan mutane ba, za ku dai sami kanku kuna gāba da Allah ne.”
Mais si elle vient de Dieu, vous ne pouvez la détruire; et prenez garde qu'il ne se trouve que vous ayez fait la guerre à Dieu.
40 Jawabinsa ya rinjaye su. Suka kira manzannin suka sa aka yi musu bulala. Sa’an nan suka kwaɓe su kada su ƙara magana a cikin sunan Yesu, suka kuma bar su suka tafi.
Et ils furent de son avis, et après avoir appelé les apôtres, et après les avoir fait fouetter, ils leur défendirent de parler au nom de Jésus; et ils les laissèrent aller.
41 Manzannin suka bar Majalisar, suna farin ciki domin an ga sun cancanta a kunyata su saboda Sunan nan.
Eux donc se retirèrent de devant le Sanhédrin, remplis de joie d'avoir été jugés dignes de souffrir des opprobres pour le nom de Jésus.
42 Kowace rana, a filin haikali da kuma gida-gida, ba su fasa koyarwa da kuma shelar labari mai daɗi cewa Yesu shi ne Kiristi ba.
Et ils ne cessaient tous les jours d'enseigner et d'annoncer Jésus-Christ, dans le temple et de maison en maison.