< Ayyukan Manzanni 5 >
1 To wani mutum mai suna Ananiyas tare da matarsa Saffiratu, shi ma ya sayar da wata mallakarsa.
Or, un homme nommé Ananias, avec Sapphira, sa femme, vendit une propriété,
2 Da cikakken sanin matarsa ya ajiye sashi daga cikin kuɗin don kansa, ya kuma kawo sauran ya ajiye a sawun manzanni.
et en retint une partie du prix; sa femme le savait aussi, puis elle en apporta une partie et la déposa aux pieds des apôtres.
3 Sai Bitrus ya ce, “Ananiyas, ta yaya Shaiɗan ya cika zuciyarka haka da ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya ka kuma ajiye wa kanka sauran kuɗin da ka karɓa na filin?
Mais Pierre dit: Ananias, pourquoi Satan a-t-il rempli ton cœur pour mentir au Saint-Esprit et pour retenir une partie du prix du terrain?
4 Ba naka ba ne kafin ka sayar da shi? Bayan da ka sayar da shi kuma, kuɗin ba naka ba ne? Me ya sa ka yi tunanin yin irin wannan abu? Ba mutum ne ka yi wa ƙarya ba, Allah ne ka yi masa.”
Tant que tu l'as gardé, n'est-il pas resté à toi? Après sa vente, n'était-elle pas en ton pouvoir? Comment se fait-il que tu aies conçu cette chose dans ton cœur? Tu n'as pas menti aux hommes, mais à Dieu. »
5 Da Ananiyas ya ji wannan, sai ya fāɗi ya mutu. Sai babban tsoro kuwa ya kama duk waɗanda suka ji abin da ya faru.
Ananias, entendant ces paroles, tomba et mourut. Une grande crainte s'empara de tous ceux qui entendirent ces choses.
6 Sai samari suka zo gaba, suka naɗe gawarsa, suka fitar da shi suka je suka binne.
Les jeunes gens, s'étant levés, l'enveloppèrent, l'emportèrent et l'ensevelirent.
7 Bayan kusan awa uku, sai matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba.
Environ trois heures après, sa femme, qui ne savait pas ce qui était arrivé, entra.
8 Bitrus ya tambaye ta ya ce, “Gaya mini, kuɗin da yake da Ananiyas kuka sayar da filin ke nan?” Ta ce, “I, haka ne muka sayar.”
Pierre lui dit: « Dis-moi si tu as vendu le terrain à un tel prix. » Elle a dit: « Oui, pour tant de choses. »
9 Bitrus ya ce mata, “Ta yaya kuka yarda ku gwada Ruhun Ubangiji? Duba! Sawun mutanen da suka binne mijinki suna bakin ƙofa, za su kuwa ɗauke ki zuwa waje ke ma.”
Mais Pierre lui dit: « Comment se fait-il que vous vous soyez mis d'accord pour tenter l'Esprit du Seigneur? Voici que les pieds de ceux qui ont enseveli ton mari sont à la porte, et ils vont te porter dehors. »
10 Nan take ta fāɗi a ƙafafunsa ta mutu. Sai samarin suka shigo ciki, suka kuwa same ta matacciya, suka ɗauke ta suka kai ta waje suka binne ta kusa da mijinta.
Elle tomba aussitôt à ses pieds et mourut. Les jeunes gens entrèrent et la trouvèrent morte; ils la portèrent dehors et l`enterrèrent près de son mari.
11 Babban tsoro ya kama dukan ikkilisiya da kuma duk wanda ya ji game da abubuwan nan.
Une grande crainte s'empara de toute l'assemblée et de tous ceux qui entendirent ces choses.
12 Manzannin suka yi ayyukan da alamu masu banmamaki masu yawa a cikin mutanen. Dukan masu bi kuwa sukan taru a Shirayin Solomon.
Par les mains des apôtres, beaucoup de signes et de prodiges se produisaient parmi le peuple. Ils étaient tous d'un commun accord sous le portique de Salomon.
13 Ba wanda ya yi karambanin shiga cikinsu, duk da haka mutane suna girmama su ƙwarai.
Aucun des autres n'osait se joindre à eux, mais le peuple les honorait.
14 Duk da haka, maza da matan da suke gaskata ga Ubangiji sai ƙaruwa suke, suka kuma ƙaru a yawa.
De plus en plus de croyants se joignaient au Seigneur, des multitudes d'hommes et de femmes.
15 A sakamakon haka, mutane suka kawo marasa lafiya a tituna suka kwantar da su a kan gadaje da tabarmai domin aƙalla inuwar Bitrus za tă bi kan waɗansunsu yayinda yake wucewa.
On transportait même les malades dans les rues et on les couchait sur des lits et des matelas, afin que, lorsque Pierre passerait, son ombre au moins couvre quelques-uns d'entre eux.
16 Jama’a ma suka tattaru daga garuruwa kewaye da Urushalima suna kawo marasa lafiyarsu da kuma waɗanda mugayen ruhohi suke damun su, dukansu kuwa suka warke.
La foule s'assemblait aussi des villes voisines de Jérusalem, amenant des malades et des personnes tourmentées par des esprits impurs; et tous étaient guéris.
17 Sai babban firist da dukan abokan aikinsa, waɗanda suke na ƙungiyar Sadukiyawa suka cika da kishi.
Mais le grand prêtre se leva, ainsi que tous ceux qui étaient avec lui (c'est la secte des sadducéens), et ils furent remplis de jalousie
18 Suka kama manzannin suka sa su a kurkukun da ake sa kowa da kowa.
et mirent la main sur les apôtres, puis les mirent en prison publique.
19 Amma da dare wani mala’ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun ya fitar da su.
Mais un ange du Seigneur ouvrit de nuit les portes de la prison, les fit sortir et leur dit:
20 Ya ce, “Ku je ku tsaya a filin haikali ku sanar wa mutane cikakken saƙon wannan sabon rai.”
« Allez vous tenir debout et parlez au peuple dans le temple de toutes les paroles de cette vie. »
21 Da gari ya waye, sai suka shiga filin haikali, yadda aka faɗa musu, suka kuwa fara koyar da mutane. Sa’ad da babban firist da abokan aikinsa suka iso, sai suka kira Majalisa gaba ɗaya dukan dattawan Isra’ila, suka kuma aika kurkuku a zo da manzannin.
Après avoir entendu cela, ils entrèrent dans le temple vers l'aube et enseignèrent. Mais le grand prêtre et ceux qui étaient avec lui vinrent convoquer le conseil, avec tout le sénat des enfants d'Israël, et envoyèrent à la prison pour les faire amener.
22 Amma da dogarawan suka iso kurkukun, ba su same su a can ba. Saboda haka suka dawo suka ba da labari, suka ce,
Mais les officiers qui étaient venus ne les trouvèrent pas dans la prison. Ils revinrent et firent ce rapport:
23 “Mun iske kurkukun a kulle sosai, da masu gadi suna tsaye a bakin ƙofofin; amma da muka buɗe su, sai muka tarar ba kowa a ciki.”
« Nous avons trouvé la prison fermée et verrouillée, et les gardes debout devant les portes; mais quand nous les avons ouvertes, nous n'avons trouvé personne à l'intérieur! ».
24 Da jin wannan labari, sai shugaban masu gadin haikali da manyan firistocin suka ruɗe, suna tunanin abin da wannan al’amari zai zama.
Or, lorsque le grand prêtre, le commandant du temple et les chefs des prêtres entendirent ces paroles, ils furent très perplexes à leur sujet et sur ce qui pourrait en résulter.
25 Sai wani ya zo ya ce, “Ga shi! Mutanen da kuka sa a kurkuku suna tsaye a filin haikali suna koya wa mutane.”
Quelqu'un vint leur dire: « Voici que les hommes que vous avez mis en prison sont dans le temple, debout et enseignant le peuple. »
26 Da wannan, shugaban ya tafi tare da dogarawansa suka kawo manzannin. Sun kawo su amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada mutane su jajjefe su da duwatsu.
Alors le capitaine alla avec les officiers et les ramena sans violence, car ils craignaient que le peuple ne les lapide.
27 Da suka kawo manzannin, sai suka sa su suka bayyana a gaban Majalisar don babban firist ya tuhume su.
Quand ils les eurent amenés, ils les présentèrent au sanhédrin. Le grand prêtre les interrogea,
28 Ya ce, “Mun kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa cikin wannan suna, duk da haka kun cika Urushalima da koyarwarku, har ma kuna so ku ɗora mana laifin jinin mutumin nan.”
en disant: « Ne vous avons-nous pas strictement ordonné de ne pas enseigner en ce nom? Voici que vous avez rempli Jérusalem de votre enseignement, et vous avez l'intention de faire retomber sur nous le sang de cet homme. »
29 Bitrus da sauran manzannin suka amsa suka ce, “Dole ne mu yi wa Allah biyayya a maimakon mutane!
Mais Pierre et les apôtres répondirent: « Nous devons obéir à Dieu plutôt qu'aux hommes.
30 Allahn kakanninmu ya tā da Yesu daga matattu, wanda kuka kashe ta wurin ratayewa a bisan itace.
Le Dieu de nos pères a ressuscité Jésus, que vous avez tué en le pendant au bois.
31 Allah ya ɗaukaka shi zuwa hannun damansa a matsayin Yerima da Mai Ceto don yă kawo tuba da gafarar zunubai ga Isra’ila.
Dieu l'a élevé par sa droite pour être Prince et Sauveur, pour donner la repentance à Israël et le pardon des péchés.
32 Mu shaidu ne ga waɗannan abubuwa, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya ba wa waɗanda suke yin masa biyayya.”
Nous sommes ses témoins de ces choses, ainsi que le Saint-Esprit, que Dieu a donné à ceux qui lui obéissent. »
33 Da suka ji haka, sai suka yi fushi suka so su kashe su.
Mais eux, en entendant cela, eurent le cœur serré, et ils étaient résolus à les faire mourir.
34 Amma wani Bafarisiyen da ake kira Gamaliyel, wani malamin doka, wanda dukan mutane ke girmamawa, ya miƙe tsaye a Majalisar ya umarta a fitar da mutanen waje na ɗan lokaci.
Mais quelqu'un se leva dans le sanhédrin, un pharisien nommé Gamaliel, docteur de la loi, honoré de tout le peuple, et ordonna de mettre les apôtres à l'écart pour un peu de temps.
35 Sa’an nan ya yi musu jawabi ya ce, “Mutanen Isra’ila, ku yi kula da kyau da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan.
Il leur dit: « Hommes d'Israël, prenez garde à ces hommes, à ce que vous allez faire.
36 Kwanan baya, Teyudas ya ɓullo, yana cewa wai shi wani mutum ne, kuma wajen mutane ɗari huɗu suka bi shi. Aka kuwa kashe shi, dukan masu binsa kuwa suka watse, kome ya wargaje.
Car, avant ces jours-ci, Theudas s'est levé, se faisant passer pour quelqu'un, et un certain nombre d'hommes, environ quatre cents, se sont joints à lui. Il fut tué, et tous ceux qui lui obéissaient furent dispersés et réduits à néant.
37 Bayansa, Yahuda mutumin Galili ya ɓullo a kwanakin ƙidaya, ya jagoranci mutane cikin tawaye. Shi ma aka kashe shi, dukan mabiyansa kuma aka watsar da su.
Après cet homme, Judas de Galilée se leva au temps de l'inscription, et il entraîna quelques personnes après lui. Lui aussi a péri, et tous ceux qui lui obéissaient ont été dispersés.
38 Saboda haka, a wannan batu na yanzu, ina ba ku shawara. Ku ƙyale mutanen nan! Ku bar su su tafi! Gama in manufarsu ko ayyukansu na mutum ne, ai, zai rushe.
Maintenant, je vous le dis, retirez-vous de ces hommes et laissez-les tranquilles. Car si ce conseil ou cette œuvre est le fait des hommes, il sera renversé.
39 Amma in daga Allah ne, ba za ku iya hana waɗannan mutane ba, za ku dai sami kanku kuna gāba da Allah ne.”
Mais si elle est de Dieu, vous ne pourrez pas la renverser, et l'on trouverait même que vous luttez contre Dieu! ».
40 Jawabinsa ya rinjaye su. Suka kira manzannin suka sa aka yi musu bulala. Sa’an nan suka kwaɓe su kada su ƙara magana a cikin sunan Yesu, suka kuma bar su suka tafi.
Ils furent d'accord avec lui. Ils convoquèrent les apôtres, les battirent, leur ordonnèrent de ne pas parler au nom de Jésus, et les relâchèrent.
41 Manzannin suka bar Majalisar, suna farin ciki domin an ga sun cancanta a kunyata su saboda Sunan nan.
Ils s'éloignèrent donc de la présence du sanhédrin, se réjouissant d'avoir été jugés dignes de subir l'opprobre pour le nom de Jésus.
42 Kowace rana, a filin haikali da kuma gida-gida, ba su fasa koyarwa da kuma shelar labari mai daɗi cewa Yesu shi ne Kiristi ba.
Chaque jour, dans le temple et dans les foyers, ils ne cessaient d'enseigner et de prêcher Jésus, le Christ.