< Ayyukan Manzanni 4 >
1 Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
Ko sta pa ljudstvu govorila, pristopijo k njima duhovni in poglavar tempeljna in Saduceji.
2 Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
Kteri so bili nevoljni, da učita ljudstvo in oznanjujeta v Jezusu vstajanje od mrtvih.
3 Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
In položé na nju roke, in denejo ju v ječo do jutra; kajti bil je uže večer.
4 Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
Veliko teh pa, kteri so besedo slišali, verovalo jih je; in postalo je število móž kakih pet tisoči.
5 Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
Zgodí se pa drugi dan, da se zberó njih poglavarji in starešine in pismarji v Jeruzalemu,
6 Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
In Ana véliki duhoven in Kajfa in Janez in Aleksander, in kolikor jih je bilo iz višega duhovskega rodú.
7 Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
In postavivši ju na sredo, vpraševali so: S kakošno močjó, ali v čegavo ime sta vidva to storila?
8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
Tedaj Peter, napolnivši se Duha svetega, reče jim: Poglavarji naroda in starešine!
9 In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
Če naju danes izprašujete za dobroto, ktero sva storila bolnemu človeku, kako je on ozdravel:
10 to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
Bodi na znanje vsem vam, in vsemu ljudstvu Izraelovemu, da v ime Jezusa Kristusa Nazarečana, kterega ste vi križali, kterega je Bog obudil iz mrtvih, po tem stoji ta pred vami zdrav.
11 Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
Ta je kamen, kterega ste vi zidarji zavrgli, kteri je postal glava oglu.
12 Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
In v nikomer drugem ni zveličanja; kajti ni ga drugega imena pod nebom danega ljudém, po kterem bi se mi mogli zveličati.
13 Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
Videč pa srčnost Petrovo in Janezovo, in vedoč, da sta neučena in priprosta človeka, čudili so se; in poznali so ju, da sta z Jezusom bila.
14 Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
In videč človeka, kteri je ozdravel, da stojí ž njima, niso kaj imeli zoper reči.
15 Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
In zapovedó jima, naj odideta ven iz zbora, in posvetujejo se med seboj,
16 Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
Govoreč: Kaj bomo storili tema človekoma? kajti da se je znani čudež po njima zgodil, znano je vsem, kteri prebivajo v Jeruzalemu, in ne moremo utajiti.
17 Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
Ali da se ne razglasí dalje med ljudstvom, zapretimo jima, naj nobenemu človeku več ne govorita o tem imenu.
18 Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
In poklicavši ju, zapovedó jima, naj nikoli več ne govorita in učita v ime Jezusovo.
19 Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
A Peter in Janez odgovarjajoč jim, rečeta: Sodite, je li prav pred Bogom, da bi vas bolj poslušala, nego Boga.
20 Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
Ne moreva namreč, da tega, kar sva videla in slišala, ne bi govorila.
21 Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
Oni pa, zapretivši jima, izpusté ju, ko niso nahajali, kako bi ju kaznovali, za voljo ljudstva, ker so vsi hvalili Boga za to, kar se je zgodilo.
22 Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
Imel je namreč več nego štirideset let ta človek, na kterem se je zgodil ta čudež ozdravljenja.
23 Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
Ko so ju pa izpustili, prideta k svojim, in povesta jim, kaj so jima véliki duhovni in starešine rekli.
24 Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
Oni pa, ko so to slišali, povzdignejo ene misli glas k Bogu, in rekó: Gospod, ti Bog, ki si ustvaril nebo in zemljo in morje in vse, kar je v njih;
25 Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
Kteri si z ustmi Davida hlapca svojega rekel: "Za kaj so se togotili pogani, in ljudstva izmišljala prazne reči?
26 Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
Postavili so se kralji zemlje, in poglavarji so se zbrali vkupej zoper Gospoda, in zoper Kristusa njegovega."
27 Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
Zbrali so se namreč zares zoper svetega sina tvojega Jezusa, kterega si pomazilil, Herod in Pontijski Pilat s pogani in ljudstvom Izraelovim,
28 Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
Da storé, kar je roka tvoja in sklep tvoj sklenil, da naj se zgodí.
29 Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
In sedaj, Gospod, poglej na njih pretenje, in daj hlapcem svojim, da bodo z vso srčnostjo govorili besedo tvojo,
30 Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
S tem, da stegneš roko svojo na uzdravljanje, in da se znamenja in čudeži godé po imenu svetega sina tvojega Jezusa.
31 Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
In ko so odmolili, potrese se mesto, na kterem so bili zbrani, in vsi se napolnijo Duha svetega, in govorili so besedo Božjo srčno.
32 Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
A množica teh, kteri so verovali, bila je enega srca in enega duha; in nihče ni govoril, da je od tega, kar je imel, njegovega kaj, nego vse jim je bilo občno.
33 Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
In z veliko močjó so dajali pričevanje aposteljni za vstajenje Gospoda Jezusa, in milost velika je bila na vseh njih.
34 Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
Ni ga bilo namreč ubogega med njimi. Kajti kolikor jih je bilo, kteri so imeli njive ali hiše, prodajali so, in donašali so ceno tega, kar so prodali,
35 su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
In pokladali so aposteljnom pred noge; in delilo se je vsakemu, kakor je kdo potreboval.
36 Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
Jozej pa, kteremu so aposteljni priimek Barnaba dali (kar se tolmači: Sin tolažbe), Levit, iz Cipra po rodu,
37 ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.
Ker je imel njivo, prodal je, in prinesel je ceno, in položil je aposteljnom pred noge.