< Ayyukan Manzanni 4 >
1 Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
While they were saying this to the people, the Priests, the Commander of the Temple Guard, and the Sadducees came upon them,
2 Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
highly incensed at their teaching the people and proclaiming in the case of Jesus the Resurrection from among the dead.
3 Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
They arrested the two Apostles and lodged them in custody till the next day; for it was already evening.
4 Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
But many of those who had listened to their preaching believed; and the number of the adult men had now grown to be about 5,000.
5 Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
The next day a meeting was held in Jerusalem of their Rulers, Elders, and Scribes,
6 Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
with Annas the High Priest, Caiaphas, John, Alexander, and the other members of the high-priestly family.
7 Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
So they made the Apostles stand in the centre, and demanded of them, "By what power or in what name have you done this?"
8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
Then Peter was filled with the Holy Spirit, and he replied, "Rulers and Elders of the people,
9 In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
if we to-day are under examination concerning the benefit conferred on a man helplessly lame, as to how this man has been cured;
10 to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
be it known to you all, and to all the people of Israel, that through the name of Jesus the Anointed, the Nazarene, whom you crucified, but whom God has raised from among the dead-- through that name this man stands here before you in perfect health.
11 Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
This Jesus is the Stone treated with contempt by you the builders, but it has been made the Cornerstone.
12 Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
And in no other is the great salvation to be found; for, in fact, there is no second name under Heaven that has been given among men through which we are to be saved."
13 Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
As they looked on Peter and John so fearlessly outspoken--and also discovered that they were illiterate persons, untrained in the schools--they were surprised; and now they recognized them as having been with Jesus.
14 Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
And seeing the man standing with them--the man who had been cured--they had no reply to make.
15 Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
So they ordered them to withdraw from the Sanhedrin while they conferred among themselves.
16 Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
"What are we to do with these men?" they asked one another; for the fact that a remarkable miracle has been performed by them is well known to every one in Jerusalem, and we cannot deny it.
17 Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
But to prevent the matter spreading any further among the people, let us stop them by threats from speaking in the future in this name to any one whatever."
18 Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
So they recalled the Apostles, and ordered them altogether to give up speaking or teaching in the name of Jesus.
19 Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
But Peter and John replied, "Judge whether it is right in God's sight to listen to you instead of listening to God.
20 Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
As for us, what we have seen and heard we cannot help speaking about."
21 Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
The Court added further threats and then let them go, being quite unable to find any way of punishing them on account of the people, because all gave God the glory for the thing that had happened.
22 Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
For the man was over forty years of age on whom this miracle of restoration to health had been performed.
23 Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
After their release the two Apostles went to their friends, and told them all that the High Priests and Elders had said.
24 Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
And they, upon hearing the story, all lifted up their voices to God and said, "O Sovereign Lord, it is Thou who didst make Heaven and earth and sea, and all that is in them,
25 Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
and didst say through the Holy Spirit by the lips of our forefather David Thy servant, "'Why have the nations stamped and raged, and the peoples formed futile plans?
26 Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
The kings of the earth came near, and the rulers assembled together against the Lord and against His Anointed.'"
27 Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
"They did indeed assemble in this city in hostility to Thy holy Servant Jesus whom Thou hadst anointed--Herod and Pontius Pilate with the Gentiles and also the tribes of Israel--
28 Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
to do all that Thy power and Thy will had predetermined should be done.
29 Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
And now, Lord, listen to their threats, and enable Thy servants to proclaim Thy Message with fearless courage,
30 Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
whilst Thou stretchest out Thine arm to cure men, and to give signs and marvels through the name of Thy holy Servant Jesus."
31 Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
When they had prayed, the place in which they were assembled shook, and they were, one and all, filled with the Holy Spirit, and proceeded to tell God's Message with boldness.
32 Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
Among all those who had embraced the faith there was but one heart and soul, so that none of them claimed any of his possessions as his own, but everything they had was common property;
33 Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
while the Apostles with great force of conviction delivered their testimony as to the resurrection of the Lord Jesus; and great grace was upon them all.
34 Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
And, in fact, there was not a needy man among them, for all who were possessors of lands or houses sold them, and brought the money which they realised,
35 su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
and gave it to the Apostles, and distribution was made to every one according to his wants.
36 Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
In this way Joseph, whom the Apostles gave the name of Bar-nabas--signifying 'Son of Encouragement' --a Levite, a native of Cyprus,
37 ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.
sold a farm which he had, and brought the money and gave it to the Apostles.