< Ayyukan Manzanni 4 >
1 Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
And while they were speaking to the people, the priests, the captain of the temple guard, and the Sadducees, came upon them;
2 Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
being grieved that they taught the people, and announced, through Jesus, the resurrection from the dead.
3 Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
And they laid hands on them, and committed them into custody to the next day; for it was now evening.
4 Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
But many of those who had heard the word, believed: and the number of the men was about five thousand.
5 Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
And the next day their rulers, elders, and scribes, gathered together at Jerusalem:
6 Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
both Annas, the high priest, and Caiaphas; also John, and Alexander, and as many as were of the high priest's kindred.
7 Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
And having set them in the midst, they inquired, By what power, or in what name, have you done this?
8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
Then Peter, full of the Holy Spirit, said to them, Rulers of the people, and elders of Israel;
9 In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
if we are this day examined about the benefit conferred on the impotent man, by what means he is healed;
10 to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
be it known to you all, and to all the people of Israel, that through the name of Jesus Christ of Nazareth, whom you crucified, whom God has raised from the dead: yes, by HIM this man stands before you hale.
11 Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
This is the stone which was set at nought by you builders, that is become the head of the corner:
12 Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
and there is salvation in no other; for there is no other name under heaven given among men, by which we can be saved.
13 Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
Now, when they saw the boldness of Peter and John, and understood that they were illiterate men, and in private stations in life, they were astonished, and recollected their having been with Jesus.
14 Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
And seeing the man that was cured standing with them, they had nothing to say against it.
15 Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
But having ordered them to withdraw out of the council, they conferred among themselves,
16 Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
saying, What shall we do with these men? for that indeed a signal miracle has been wrought by them, is manifest to all the inhabitants of Jerusalem; and we can not deny it.
17 Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
Nevertheless, that it may not spread any further among the people, let us charge them, with the severest threats, to speak no more to any man in this name.
18 Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
And having called them, they charged them neither to speak nor teach any more in the name of Jesus.
19 Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
But Peter and John, answering them, said, Whether it be just in the sight of God, to obey you rather than God, judge you:
20 Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
for we can not but speak the things which we have seen and heard.
21 Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
And having threatened them again, they dismissed them, on account of the people, finding nothing for which they might punish them; because all the people glorified God for that which was done;
22 Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
for the man on whom this miracle of healing was wrought, was more than forty years old.
23 Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
And being dismissed, they came to their own company, and related all that the chief priests and elders had said to them.
24 Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
And when they heard it, they lifted up their voice with one accord to God, and said, Lord, thou art the God who didst make heaven and earth; and the sea, and all things that are in them:
25 Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
who didst say by the mouth of thy servant David, "Why did the heathen rage, and the people imagine vain things?
26 Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
The kings of the earth set themselves, and the rulers combined together against the Lord, and against his anointed."
27 Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
For of a truth, against thy holy Son Jesus, whom thou hast anointed, both Herod, and Pontius Pilate, with the heathen, and the people of Israel,
28 Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
have combined to do what thy hand and thy counsel marked out before to be done.
29 Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
And now, O Lord, regard their threatenings; and give to thy servants to speak thy word with all freedom;
30 Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
whilst thou stretchest out thy hand to heal, and signs and wonders are doing through the name of thy holy Son Jesus.
31 Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
And while they were praying, the place in which they were assembled was shaken: and they were all filled with the Holy Spirit, and they spoke the word of God with freedom.
32 Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
Now the heart and soul of the multitude of believers was one: nor did any one call any of his possessions his own; but all things were common among them.
33 Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
And with great power did the Apostles give forth their testimony concerning the resurrection of the Lord Jesus: and great kindness was among them all.
34 Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
Neither was there one indigent person among them; for as many as were proprietors of lands or houses, sold them, and brought the price of the things they sold,
35 su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
and laid it down at the feet of the Apostles: and distribution was made to each according to his need.
36 Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
And Joses, who, by the Apostles, was surnamed Barnabas, (which being interpreted, signifies a Son of Exhortation, ) a Levite, and by birth a Cyprian,
37 ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.
having an estate, sold it, and brought the money and laid it down at the feet of the Apostles.