< Ayyukan Manzanni 4 >
1 Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
And they speaking to the people, the priests and captain of the temple and the Sadducees rose up against them,
2 Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
being grieved because they were teaching the people and preaching the resurrection of the dead through Jesus;
3 Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
and they laid hands on them and put them in prison till the morrow; for it was already evening.
4 Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
And many of those hearing the word believed, and the number of men was about five thousand.
5 Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
And it came to pass on the morrow, the rulers and elders and scribes
6 Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
assembled in Jerusalem, and Annas the high priest and Caiaphas and John and Alexander, and so many as were of the family of the high priest.
7 Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
And having set them in the midst, asked them, By what power or in what name have you done this?
8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
Then Peter being full of the Holy Spirit said to them, Ye rulers of the people and elders,
9 In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
if we are this day judged for the benefaction of the impotent man, by whom he has been saved,
10 to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
let it be known to you all, and to all the people of Israel, that in the name of Jesus Christ, the Nazarene whom you crucified, whom God raised from the dead, through him this man now stands sound in your presence.
11 Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
This is the stone rejected by your builders, which has become the head of the corner.
12 Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
And there is salvation in no other; for there is no other name given under heaven among men by which it behooveth us to he saved.
13 Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
And seeing the boldness of Peter and John, and apprehending that they are unlearned and ignorant men, they continued to be astonished, and recognized them, that they were with Jesus;
14 Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
and seeing the man who had been healed standing with them, they had nothing to say against it.
15 Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
And having commanded them to depart out from the assembly, they conferred with one another,
16 Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
saying, What can we do to these men? for that a notable miracle has been wrought by them is indeed manifest to all dwelling at Jerusalem, and we are not able to deny it;
17 Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
but that it may extend no further unto the people, let us threaten them to speak no more in this name to any one of men.
18 Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
And having called them, they command them, not at all to speak or teach in the name of Jesus.
19 Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
And Peter and John responding said to them, Whether it is right in the sight of God to hearken unto you rather than God, judge ye;
20 Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
for we are not able not to speak those things which we have seen and heard.
21 Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
And they having threatened them, in addition sent them away, finding nothing to the end that they can punish them, on account of the people, because all continued to glorify God over that which had taken place;
22 Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
for the man on whom this miracle of healing was wrought was more than forty years old.
23 Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
And having been released they came to their own people, and proclaimed so many things as the chief priests and elders said to them.
24 Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
And having heard, they unanimously lifted up their voice to God, and said, O Lord, thou having created the heaven and the earth and the sea and all things which are in them,
25 Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
the One speaking through the mouth of David, thy child, our father through the Holy Ghost, Wherefore did the heathen rage, and the people imagine vain things?
26 Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
The kings of the earth stood up, and the rulers were gathered together against the Lord and his Christ.
27 Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
For in truth they were assembled together in this city, against thy holy Child Jesus, whom thou didst anoint; both Herod and Pontius Pilate, with the Gentiles and the people of Israel,
28 Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
to do so many things as thy hand and thy counsel did foreordain to come to pass.
29 Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
And now, Lord, look upon their threats and grant to thy servants with all boldness to speak thy word,
30 Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
while, reaching forth thy hand unto healings, both miracles and wonders are wrought through the name of thy holy child Jesus.
31 Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
And they praying, the place in which they were assembled was shaken, and they were all filled with the Holy Ghost, and continued to speak the word of God with boldness.
32 Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
And of the multitude who believed there was one heart and soul, and no one was saying that any of those things which belonged to him were his own, but all things were common to them.
33 Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
And with great power the apostles continued to give witness of the resurrection of Jesus Christ the Lord; and great grace was upon them all.
34 Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
For no one among them was in need; for so many possessions of lands or houses as belonged to them, selling, they were bringing the prices of the things having been sold,
35 su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
and laying them at the feet of the apostles; and it was distributed to each as any one had need.
36 Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
And Joseph called Barnabas by the apostles, which is interpreted, Son of consolation, a Levite, a Cyprian by race,
37 ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.
a farm belonging to him, having sold it, he brought the money and laid it at the feet of the apostles.