< Ayyukan Manzanni 3 >
1 Wata rana, Bitrus da Yohanna suna haurawa zuwa haikali a lokacin addu’a da ƙarfe uku na rana.
[One day] Peter and John were going to the Temple [courtyard]. It was three o’clock in the afternoon, which was the time when people prayed [there publicly].
2 To, sai ga wani da aka haifa gurgu ana ɗauke da shi zuwa ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, inda akan ajiye kowace rana, don yă yi bara daga masu shigowa cikin filayen haikali.
There was a man there who had been lame from the time he was born. He [was sitting by] the gate called Beautiful [Gate], at the entrance to the Temple [area]. People put him there every day, so that he could ask those who were entering [or leaving] the temple courtyard to give him some money.
3 Da ya ga Bitrus da Yohanna suna gab da shiga, sai ya roƙe su kuɗi.
As Peter and John were about to enter [the Temple courtyard], the lame man saw them and asked them several times to give him some money. (OR, The lame man said to them several times, “Please give me some money!”)
4 Bitrus kuwa ya kafa masa ido, haka ma Yohanna. Sai Bitrus ya ce, “Dube mu!”
As Peter and John looked directly at him, Peter said to him, “Look at us!”
5 Saboda haka mutumin ya mai da hankalinsa a kansu, yana fata samun wani abu daga gare su.
So he looked directly at them, expecting to get some [money] from them.
6 Sai Bitrus ya ce, “Azurfa ko zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. A cikin sunan Yesu Kiristi Banazare, ka yi tafiya.”
Then Peter said to him, “I do not have any money [MTY], but what I [can do], I will [do] for you. Jesus Christ, [who was] from Nazareth [town], has authorized [MTY] me [to heal you! So get up and] walk!”
7 Ta wurin kama hannunsa na dama, ya taimake shi ya miƙe, nan take ƙafafu da idon sawun mutumin suka yi ƙarfi.
Then Peter grasped the man’s right hand and helped him to stand up. Immediately the man’s feet and ankles became strong.
8 Sai ya yi wuf da ƙafafunsa ya fara tafiya. Ya tafi tare da su ya shiga cikin filin haikali yana tafiya yana tsalle, yana kuma yabon Allah.
He jumped up and began to walk! Then he entered the Temple [area] with them, walking and leaping and praising God!
9 Sa’ad da dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana yabon Allah,
All the people [there] saw that man walking and praising God.
10 sai suka gane cewa shi ne mutumin nan wanda dā yake zama yana bara a bakin ƙofar haikalin da ake kira Kyakkyawa, suka kuwa cika da mamaki da tsoro a kan abin da ya faru gare shi.
They recognized that he was the man who used to sit at the Beautiful Gate in the Temple [courtyard] and ask [people] for money! So all the people there were greatly amazed at what had happened to him.
11 Tun mai bawan yana riƙe da Bitrus da Yohanna, dukan mutanen suka yi mamaki, suka zo wurinsu a guje a inda ake kira Shirayin Solomon.
As the man clung to Peter and John, all the people were so surprised [that they did not know what to think] So they ran to the two apostles at the place [in the Temple courtyard] that is called {that [people] call} Solomon’s Porch.
12 Da Bitrus ya ga haka, sai ya ce musu, “Mutanen Isra’ila, don me wannan ya ba ku mamaki? Don me kuke kallonmu sai ka ce da ikon kanmu ne ko kuwa don ibadarmu ne muka sa wannan mutum ya yi tafiya?
When Peter saw that, he said to the crowd, “Fellow Israelites, (you should not be surprised about what has happened to this man!/why are you so surprised about what has happened to this man?) [RHQ] And you should not stare at us, either! You seem to [RHQ] think that the two of us enabled this man to walk because we [(exc)] ourselves are powerful or because we please God very much!
13 Allah na Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub, Allah na kakanninmu, ya ɗaukaka bawansa Yesu. Ku kuka ba da shi domin a kashe, kuka yi mūsun saninsa a gaban Bilatus, ko da yake ya yi niyya ya sake shi.
[So I will tell you what is really happening]. Our ancestors, including Abraham, Isaac, and Jacob, worshipped God. And now he has greatly honored Jesus, who always served him. Your [leaders] brought Jesus [to the governor, Pilate], so that [his soldiers would kill him]. And [God considers that] in front of Pilate you [were the ones who rejected] Jesus [as your king], after Pilate had decided that he should release Jesus.
14 Kuka yi mūsun sanin Mai Tsarki da Mai Adalci kuka roƙa a sakar muku mai kisankai.
[Although Jesus] always did what was right/just and good, you rejected him. [Pilate wanted to release him, but] you urgently asked Pilate to release (a murderer/someone who had killed people)!
15 Kuka kashe tushen rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu. Mu shaidu ne ga wannan.
[God considers that] you killed [Jesus], the one who gives people [eternal] life. But God has greatly honored him (by causing him to become alive again after he died/by raising him from the dead). Many of us saw [him after that, and now] we [(exc)] are telling [you] about it.
16 Ta wurin bangaskiya cikin sunan Yesu ne wannan mutum da kuke gani kuka kuma sani ya sami ƙarfi. Da sunan Yesu, da kuma bangaskiyar da take samuwa ta wurinsa ne ya ba shi cikakkiyar warkarwa, yadda dukanku kuke gani.
It is because [we two] trusted in what Jesus [MTY, PRS] [could do, that he] made this man, whom you see and know, strong again. Yes, it is because we [(exc)] trusted in Jesus that he has completely healed this man for all of you to see.”
17 “To,’yan’uwa, na san cewa, kun aikata wannan cikin jahilci ne, yadda shugabanninku suka yi.
“Now, my fellow-countrymen, I know that you and your leaders did that [to Jesus] because you [and they] did not know [that he was the Messiah].
18 Amma ta haka ne Allah ya cika abin da ya rigyafaɗi ta bakin dukan annabawa cewa, Kiristinsa zai sha wahala.
However, [your putting him to death] was what God had predicted that people would do. [Long ago] he told all the prophets [MTY] to write [what people would do to the Messiah. They wrote] that the Messiah, whom God [would send], would suffer [and die].
19 Saboda haka ku tuba, ku juyo ga Allah, don a shafe zunubanku, don lokutan wartsakewa su zo daga wurin Ubangiji,
So, turn away from your sinful behavior and ask God [to help you] do what pleases [him], in order that he may completely forgive you for your sins.
20 don kuma ya iya aika da Kiristi, wanda aka naɗa tun dā saboda ku, Yesu ke nan.
[If you do that], there will be times [when you will know that] the Lord [God is] helping [you]. And some day he will [again] send back [to earth] the Messiah, whom he appointed for you. That person is Jesus.
21 Dole yă kasance a sama, sai lokaci ya yi da Allah zai mai da kome sabo, yadda ya yi alkawari tun dā ta wurin annabawansa masu tsarki. (aiōn )
Jesus must stay in heaven until the time when God will cause all that he has created to become new. Long ago God promised [to do that, and] he chose holy prophets to tell [that to people]. (aiōn )
22 Gama Musa ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai tasar muku wani annabi kamar ni daga cikin mutanenku; dole ku saurari duk abin da ya faɗa muku.
For [example, the prophet] Moses said [this about the Messiah]: ‘The Lord (your God/the God whom you [worship]) will cause someone to become a prophet to tell you [God’s message. God will send him] as [he sent] me, [and he will be] from among your own people. You must listen to everything that this prophet tells you [and obey him] [SYN].
23 Duk wanda bai saurare shi ba za a ware shi gaba ɗaya daga mutanensa.’
[Those who] do not listen to [that prophet and obey] him will no longer belong to God’s people, and [God] will get rid of them’.”
24 “Tabbatacce, dukan annabawa daga Sama’ila zuwa gaba, dukansu da suka yi magana, sun rigya faɗin waɗannan kwanaki.
[Peter continued], “All the prophets have told [about what would happen during] the time [MTY] [in which we(inc) are living. Those prophets include] Samuel [and all the others who] later also spoke [about these events] before they happened.
25 Ku kuwa magādan annabawan ne da kuma na alkawarin da Allah ya yi da kakanninku. Ya ce wa Ibrahim, ‘Ta wurin zuriyarka, dukan kabilan duniya za su sami albarka.’
You [as well as we(exc)] are the people [to whom God sent the Messiah, as] the prophets said [MTY] [that he would]. And when God strongly promised [to bless] our ancestors, he also surely promised to bless you. He said to Abraham [concerning the Messiah], ‘[I] will bless all people on the earth as a result of [what] your descendant [will do].’”
26 Da Allah ya tashe bawansa, ya aike shi da fari zuwa gare ku don yă albarkace ku ta wurin juye kowannenku daga mugayen hanyoyinku.”
[Peter concluded], “[So] when God sent [to the earth] (Jesus, the one who always obeys him/his servant Jesus), he sent him first to you [Israelites] to bless you. [God will] enable you to stop doing what is wicked [and to start doing what pleases him].”